Sanata Barau Ya Kai Ziyarar Gani Da Ido Aikin Da Ake Yi A AKTH
Published: 20th, October 2025 GMT
Gwamnatin Tarayya ta sake jaddada kudirinta na inganta harkar kiwon lafiya a fadin kasar nan, daidai da manufar sabunta kudiri na Shugaba Bola Ahmed Tinubu, wato Renewed Hope Agenda.
Wannan tabbacin ya fito ne daga Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, yayin da yake ziyarar duba ayyukan gine-gine da ke gudana a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH), wanda shi ne ya tallafa wajen samar da su.
Yayin da yake magana da ’yan jarida a lokacin ziyarar, Sanata Barau ya ce wadannan ayyuka na da nufin kara karfin cibiyoyin kiwon lafiya a cikin gida, tare da rage yawan tafiyar da ake yi zuwa kasashen waje domin neman magani, ta hanyar samar da ingantattun kayan aiki a asibitocin cikin gida.
“Wadannan shirye-shirye suna cikin cikakkiyar manufa ta Shugaba Tinubu ta farfado da sashen kiwon lafiya,” in ji shi. “Nigeria na da kwararrun ma’aikatan lafiya, kuma idan aka samar musu da ingantattun kayan aiki, za a karfafa gwiwarsu, kuma za mu iya cimma burin kasa wajen ingantaccen tsarin kiwon lafiya.”
Dan majalisar ya kara da cewa, idan an kammala wadannan ayyuka, za su taimaka wajen kara ingancin ayyukan asibitin, tare da bai wa jama’a damar samun kulawar lafiya ta zamani da inganci.
A nasa bangaren, Babban Daraktan Asibitin, Farfesa Abdulrahman Sheshe, ya nuna godiya bisa wannan taimako, yana mai cewa ayyukan suna tafiya yadda ya kamata, kuma ana sa ran kammalawa da kaddamar da su kafin shekarar 2026.
A cewarsa, ayyukan sun hada da gina Cibiyar Nazarin Cutar Zuciya da Kwakwalwa (Cardio-Cerebral Center), Cibiyar Kula da Yara (Pediatric Center), da masaukan daliban jinya, da sauran muhimman gine-gine.
“Wadannan sabbin cibiyoyi za su kara yawan gadon marasa lafiya, kuma za su ba mu damar gudanar da ayyukan da ba mu iya yi ba a baya,” in ji Farfesa Sheshe.
Ya kara da cewa, sabbin cibiyoyin za su kara ingancin ayyuka, tare da karfafa matsayin asibitin wajen zama jagora a harkar kiwon lafiya a yankin.
Abdullahi Jalaluddeen
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: kiwon lafiya
এছাড়াও পড়ুন:
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna
Ƴansandan sun kuma yi kira ga ƴan jarida da su tabbatar da daidaito a rahotanninsu, tare da tuntuɓar sashin hulɗa da jama’a na yankin kafin yaɗa labaran da ke da sarƙakiya. AIG Garba ya gargaɗi ƴan jarida da su guji tsoma baki a cikin binciken da ke gudana, yana mai cewa “a bar doka ta yi aikinta.”
Sai dai sanarwar ba ta fayyace halaccin tsarewar farko da aka yi wa ɗan jaridar ba, ko kuma ko an kama shi ne ba tare da takardar izinin kame ba.
A halin yanzu, ƙungiyoyin kare ƴancin ƴan jarida da ƙungiyoyin farar hula da dama suna ci gaba da kira ga ƴansanda da su saki Ishaq tare da dakatar da duk wani yunƙuri na tsoratar da ƴan jarida daga gudanar da aikinsu cikin ƴanci.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA