Aminiya:
2025-10-20@16:25:02 GMT

Kano Pillars ta dakatar da Kocinta

Published: 20th, October 2025 GMT

Hukumar gudanarwar Kungiyar Kwallon kafa ta Kano Pillars ta dakatar da Babban Kocinta Ahmed Garba Yaro Yaro da bai ba da shawara ga  Kocin, Ogenyi Evans, nan take.

Ta kuma nada tsohon kyaftin kuma Mataimakin Koci, Gambo Muhammad nan take, ya jagoranci lamuran fasaha na ƙungiyar. Mai horar da masu tsaron raga, Suleiman Shuaibu, zai taimaka masa, yayin da Koci Garzali Muhammad (Kusa) daga Junior Pillars zai ba da ƙarin goyon baya har sai an fitar da sabbin umarni.

Kungiyar ta dauki wannan mataki ne bayan abin da ta kira “rashin tagomashinta” a Gasar Firimiyar Najeriya (NPFL) ta 2025/2026 da ake ci gaba da yi.

Sanarwa da kulob ɗin ta fitar, hukumar gudanarwar ta ce an ɗauki matakin ne bayan nazarin yadda ƙungiyar ta yi rashin nasara a wasannin ta na baya-bayan nan.

Ta ce “Yanzu haka, ’yan wasan sun buga wasanni takwas, amma nasara biyu kacal suka samu a ciki, sun yi canjaras biyu, sannan kuma an doke su a wasanni huɗu.”

An kama ɗan uwan Nnamdi Kanu da lauyansa —Sowore Juyin mulki: Ana zargin tsohon gwamna da ɗaukar nauyin sojojin Najeriya

Kulob ɗin, wanda yana ɗaya daga cikin ƙungiyoyin da suka fi rawar gani a tarihin ƙwallon ƙafa a Najeriya, yana fama da rashin daidaituwa a wannan kakar, abin da ke tayar da hankalin magoya baya da masu ruwa da tsaki kan jagorancin ƙungiyar.

Sanarwar ta tabbatar wa magoya baya cewa hukumar gudanarwar ta ci gaba da jajircewa wajen dawo da ƙungiyar kan turba da kuma dawo da dabi’ar ta ta samun nasara.

Kano Pillars, wadda aka fi sani da ‘Sai Masu Gida’, a halin yanzu tana can ƙasan teburin gasar ta NPFL, kuma tana fatan samun canji mai kyau yayin da kakar ke ci gaba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: dakatar da koci Kano Pillars

এছাড়াও পড়ুন:

Al-Houthi: Matsin lamba bai hana Iran ci gaba da goyon bayan Falasdinu

Shugaban kungiyar Ansarullah ta kasar Yaman Sayyid Abdul-Malik Badreddin al-Houthi ya yi jawabi a yammacin yau alhamis kan batutuwa daban-daban da suka shafi duniyar musulmi, musamman abubuwan da suka faru a Gaza da Yemen. Ya ci gaba da cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran, ba tare da la’akari da duk wani matsin lamba ba, ta yi sadaukarwa ta karshe a kan turbar goyon bayan Falasdinu, kuma ta bayar da dama ga kwamandojin gwagwarmayar ‘yanci, daga cikinsu akwai babban kwamandan shahidi Qassem Soleimani.

Yayin da yake magana kan zagayowar shahadar babban kwamanda Yahya al-Sinwar, Sayyid Abdul-Malik Badreddin ya ce: “Babban darussan da ya bari na tsararraki, da kuma matsayinsa na sadaukar da kai da jihadi, suna wakiltar muhimman dabi’u da kuma babban matakin wayar da kan jama’a, wanda hakan ya samar da wata mazhaba mai karfafa gwiwa ga tsararraki.

Har ila yau jagoran Ansarullah ya mika sakon taya murna da ta’aziyyar shahadar shahidan Ghamari (Babban Hafsan Sojin Yaman) zuwa ga iyalansa, da ‘yan uwansa, da dukkan ‘yan’ yanci. Ya kara da cewa, Shahidai al-Ghamari ya taka rawa sosai wajen tallafawa Gaza, kuma tun bayan shahadarsa ‘yan uwansa suka ci gaba da yin jihadi.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Marzieh Jafari  Ta Dauki Lambar Yabo Ta Horar Da Mata Wasan Kwallon Kafa Ta Nahiyar Asia October 18, 2025 Iran: Kudurin Kwamitin Tsaro Kan Yarjeniyar JCPOA Ya Kawo Karshe A Yau October 18, 2025 Iran: Kauyuka 3 Sun Shiga Cikin Wuraren Bude Ido Na Duniya October 18, 2025 Aref: Kofar Tattaunawa A Bude Take, Amma Ba Zamu Amince Da Bukatun Da Basa Da Ma’an Ba October 18, 2025 Kenya Ta Yiwa Raila Odinga Jana’iza Ta Musamman October 18, 2025 Kwamandan Rundunar Kudancin Amurka ya sanar da murabus kan  batun  ayyukan soji a yankin Caribbean October 18, 2025 Janar Sulaimani: A Yayin Yakin Kwanaki 12 Iran Ta Tarwatsa Wasu Muhimman Wurare 21 Na Isra’ila October 17, 2025 Abokan Yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya Sun Ce: Sake Dawo Da Takunkumin Da Aka Kakaba Kan Iran Baya Kan Doka October 17, 2025 Iran Ta Yi Allah Wadai Da Wuce Gona Da Irin Isra’ila Kan Kudancin Kasar Lebanon October 17, 2025 Kungiyar Hamas Ta Yi Kira Da Matsa Wa Isra’ila Lamba Da Ta Cika Sharuddan Yarjejeniyar Gaza October 17, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dembele ya dawo PSG bayan jinyar makonni
  • Yadda Morocco ta kafa tarihin ɗaga Kofin Duniya na FIFA U20
  • Kano Pillars Ta Dakatar Da Babban Kocinta Bisa Rashin Katabus A Kakar Wasa Ta NPFL
  • Kano Pillars Ta Dakatar Da Manyan Masu Horas Da ‘Yan Wasanta Saboda Rashin Nasara
  • NAJERIYA A YAU: Shin Ya Kamata A Saki Shugaban IPOB Nnamdi Kanu?
  • Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu
  • Talauci ne babban maƙiyin ɗan Adam — Atiku
  • Al-Houthi: Matsin lamba bai hana Iran ci gaba da goyon bayan Falasdinu
  • Ta’addanci: An fi kashe Musulmi a kan Kiristoci a Najeriya — Jakadan Amurka