Assalamu alaikum masu sauraro sharhin bayan labarammu zai yi magana dangane da ‘Atisayen sojojin ruwa mai taken (“damarar tsaro na shekara ta 2025”) wandake ke gudana a nan Iran. Wanda ni tahir amin zan karanta.

////.. A ranar litinin da ta gabata ce sojojin ruwa na kasashen China, Rasha da kuma Iran suka fara atisayen sojojin ruwa na hadin giwan kasashen uku, wanda suka sanya masa suna :damarar tsaro na shekara ta 2025″ wanda kuma ke gudana a halin yanzu a arewacin tekun Indiya da ke kudu maso gabacin kasar Iran da tekun farisa da kuma tekun Omman.

Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya bayyana cewa atisayen wanda zai dauki kwanaki uku cur ana gudanar da shi, zai maida hankali wajen al-amuran da suka shafi tsaron ruwa na yankuna daban-daban a inda wadanda kasashe suke kula da su.

Labarin ya kara da cewa a yau talata sojojin kasashen uku sun gudanar da wani bangare na atisayen. Rear admiral Mostafa Tajeddine mataimakin kwamandan gudanarwa na sojojin Ruwa na kasar Iran ne ya bayyana haka. Ya kuma kara da cewa wannan bangaren daukar hotuna na atisayen ya kammala kamar yadda aka tsara.

Tajuddine ya kara da cewa ana daukar hotunan yadda atisayen ke gudana daga jirgin ruwa wanda yake kula da hakan daga cikin jiragen ruwan yaki sojojin ruwa na rundunar IRGC. Ya kuma ce JMI tana da shirin kula da zaman lafiya a yankunan ruwa daban –daban a kasashe yankin da kuma na sauran kasashen duniya.

Shi ma a jawabinsa Rear admiral Shahram Irani, babban kwamandan sojojin Ruwa na JMI ya bayyana cewa, yayi watsi da zancen shugaban kasar Amurka Donal Trump dangane da wannan atisayen na cewa, Amurka tafi taron kasashen Iran Rasha da kuma China, ya kuma bayyana cewa wannan kalaman ‘rudu ne’ kawai wanda shugaban ya shiga.

Kafin haka dai shugaban  kasar na Amurka yace bai damu da atisayen kasashen uku suka yi a tekun faraisa, don ya san Amurka ta fi su karfi gaba daya. Irani ya ce manufar kasashen uku a wannan atisayen, mai suna ‘damarar tsaro na shekara ta 2025″ ita ce tabbatar da tsaro a yankin da kuma duniya, sabanin abinda Amurka take yi na samar da tashe-tashen hankula a cikinta.

Ya kuma kara da cewa, yakama ta gwamnatin Amurka ta sani, yawan kasashen da suke da karfin sojojin ruwa a duniya sun kara, kuma suna gwada karfinsu a wurare da dama a yankin Asiya da kuma wasu wurare a duniya. Ya ce kasashen kungiyar Shanghai da Brics da dama suna da karfin tabbatar da zaman lafiya a yankuna da dama a duniya. Suna da karfin ganin harkokin tattalin arziki na yankunansu da kuma kasashensu suna gudana da kyau.

Ya ce wasu kasashe banda wadannan uku, suna shirye-shiryen hadewa da wannan atisayen nan gaba. Wannan dai shi ne atisay karo na 7th wadanda wadannan kasashe uku China Iran da kuma Rasha, wanda yake karfafa kwarewarsu a tabbatar da tsaro a cikin ruwayen kasashen yankin, har’ila yau akwai wasu kasashe da dama daga yankin da kuma wasu kasashe daga nesa suna a matsayin masu kallo a wannan atisayen.

Banda haka wadannan atisayen zai hana kan wadannan kasashe don cimma manufa guda ta samar da zaman lafiya a dukkan hanyoyin zirga zirgan kasuwanci da hulda ta cikin ruwa a yankin da kuma duniya.

A cikin yan kwanakin nan ne shugaban kasar Amurka take barazanar kaiwa cibiyoyin nukliya na kasar Iran, don hanata, abinda ya kira makamin Nkliya. Ko kuma iran ta amince ta zauna da Amurka ita kadai don ta fada mata abinda zata yi, da abinda ba zatayi ba a fagen makamashin nukliya. Wanda Iran tace ba zata taba zama da Amurka don tattauna batun shirinta na makamashin nukliya ba.

Tun kafin ya sake dawowa kan kujerar shugabancin kasar Amurka, a karo na biyu, shugaban yake barzanar zai tursaswa iran ta amince don tattaunawa da ita kan shirinta na makamashin nukliya.

Amma idan ta ki amincewa zai yi amfani da karfin don wargaza shirinta na makamshin nukliya don ba zata amince iran ta mallaka makaman Nukliya ba.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: a wannan atisayen sojojin ruwa na yankin da kuma kara da cewa

এছাড়াও পড়ুন:

Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso

Tsohon Gwamnan Jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana damuwarsa kan kalaman da Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi game da Najeriya.

Kwankwaso, ya yi wannan magana ne bayan Trump ya yi barazanar ɗaukar matakin yaƙi game da zargin kisan kiyashi da ake yi wa Kiristoci.

Kisan Kiristoci: Ba zan yaƙi ƙasar iyayena kan labaran ƙarya ba — Sojan Amurka Kisan Kiristoci: Lauyoyi sun nemi Gwamnatin Tarayya ta tattauna da Amurka

A cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Kwankwaso, ya ce Najeriya ƙasa ce mai cikakken ’yanci, wadda ke fama da matsalar tsaro daga miyagu a sassa daban-daban na ƙasar.

“Matsalar tsaron da muke fuskanta ba ta bambanta tsakanin addini, ƙabila ko ra’ayin siyasa,” in ji shi.

Ya buƙaci gwamnatin Amurka da ta tallafa wa Najeriya da sabbin fasahohi domin yaƙar matsalar tsaro maimakon yin kalaman da za su iya raba kan ’yan ƙasa.

“Amurka ya kamata ta taimaka wa hukumomin Najeriya da ingantattun fasahohi don magance matsalolin tsaro, maimakon yin barazanar da za ta ƙara raba ƙasar,” in ji Kwankwaso.

Haka kuma, ya shawarci Gwamnatin Najeriya da ta naɗa jakadu na musamman domin inganta hulɗar diflomasiyya da Amurka da kare muradun ƙasar a matakin duniya.

Ya kuma yi kira ga ’yan Najeriya da su zauna lafiya, inda ya bayyana cewa wannan lokaci ne da ya dace a fifita haɗin kan ƙasa ba abin da ke raba ta ba.

“Wannan lokaci ne da ya kamata mu mayar da hankali kan abin da zai haɗa kanmu ba wanda zai raba mu ba. Allah Ya albarkaci Najeriya,” in ji shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon barazana — Kwankwaso
  • Tsaro: Taimakonmu Amurka ya kamata ta yi maimakon ba barazana ba — Kwankwaso
  • Araqchi: Da Hadin Bakin Amurka, Gwamnatin Isra’ila ta kaddamar Da Hari Kan Kasar Iran
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa
  • Sin Da Amurka Suna Taimaka Wa Juna Da Samun Wadata Tare
  • Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta
  • Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?
  • Sudan : Kasashen duniya na Allah wadai da cin zarafi a lokacin kama El-Fasher