Sharhin Dangane da: Atisayen Damarar Tsaro Ta 2025 Tsakanin Kasashen China, Rasha Da Iran
Published: 11th, March 2025 GMT
Assalamu alaikum masu sauraro sharhin bayan labarammu zai yi magana dangane da ‘Atisayen sojojin ruwa mai taken (“damarar tsaro na shekara ta 2025”) wandake ke gudana a nan Iran. Wanda ni tahir amin zan karanta.
////.. A ranar litinin da ta gabata ce sojojin ruwa na kasashen China, Rasha da kuma Iran suka fara atisayen sojojin ruwa na hadin giwan kasashen uku, wanda suka sanya masa suna :damarar tsaro na shekara ta 2025″ wanda kuma ke gudana a halin yanzu a arewacin tekun Indiya da ke kudu maso gabacin kasar Iran da tekun farisa da kuma tekun Omman.
Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya bayyana cewa atisayen wanda zai dauki kwanaki uku cur ana gudanar da shi, zai maida hankali wajen al-amuran da suka shafi tsaron ruwa na yankuna daban-daban a inda wadanda kasashe suke kula da su.
Labarin ya kara da cewa a yau talata sojojin kasashen uku sun gudanar da wani bangare na atisayen. Rear admiral Mostafa Tajeddine mataimakin kwamandan gudanarwa na sojojin Ruwa na kasar Iran ne ya bayyana haka. Ya kuma kara da cewa wannan bangaren daukar hotuna na atisayen ya kammala kamar yadda aka tsara.
Tajuddine ya kara da cewa ana daukar hotunan yadda atisayen ke gudana daga jirgin ruwa wanda yake kula da hakan daga cikin jiragen ruwan yaki sojojin ruwa na rundunar IRGC. Ya kuma ce JMI tana da shirin kula da zaman lafiya a yankunan ruwa daban –daban a kasashe yankin da kuma na sauran kasashen duniya.
Shi ma a jawabinsa Rear admiral Shahram Irani, babban kwamandan sojojin Ruwa na JMI ya bayyana cewa, yayi watsi da zancen shugaban kasar Amurka Donal Trump dangane da wannan atisayen na cewa, Amurka tafi taron kasashen Iran Rasha da kuma China, ya kuma bayyana cewa wannan kalaman ‘rudu ne’ kawai wanda shugaban ya shiga.
Kafin haka dai shugaban kasar na Amurka yace bai damu da atisayen kasashen uku suka yi a tekun faraisa, don ya san Amurka ta fi su karfi gaba daya. Irani ya ce manufar kasashen uku a wannan atisayen, mai suna ‘damarar tsaro na shekara ta 2025″ ita ce tabbatar da tsaro a yankin da kuma duniya, sabanin abinda Amurka take yi na samar da tashe-tashen hankula a cikinta.
Ya kuma kara da cewa, yakama ta gwamnatin Amurka ta sani, yawan kasashen da suke da karfin sojojin ruwa a duniya sun kara, kuma suna gwada karfinsu a wurare da dama a yankin Asiya da kuma wasu wurare a duniya. Ya ce kasashen kungiyar Shanghai da Brics da dama suna da karfin tabbatar da zaman lafiya a yankuna da dama a duniya. Suna da karfin ganin harkokin tattalin arziki na yankunansu da kuma kasashensu suna gudana da kyau.
Ya ce wasu kasashe banda wadannan uku, suna shirye-shiryen hadewa da wannan atisayen nan gaba. Wannan dai shi ne atisay karo na 7th wadanda wadannan kasashe uku China Iran da kuma Rasha, wanda yake karfafa kwarewarsu a tabbatar da tsaro a cikin ruwayen kasashen yankin, har’ila yau akwai wasu kasashe da dama daga yankin da kuma wasu kasashe daga nesa suna a matsayin masu kallo a wannan atisayen.
Banda haka wadannan atisayen zai hana kan wadannan kasashe don cimma manufa guda ta samar da zaman lafiya a dukkan hanyoyin zirga zirgan kasuwanci da hulda ta cikin ruwa a yankin da kuma duniya.
A cikin yan kwanakin nan ne shugaban kasar Amurka take barazanar kaiwa cibiyoyin nukliya na kasar Iran, don hanata, abinda ya kira makamin Nkliya. Ko kuma iran ta amince ta zauna da Amurka ita kadai don ta fada mata abinda zata yi, da abinda ba zatayi ba a fagen makamashin nukliya. Wanda Iran tace ba zata taba zama da Amurka don tattauna batun shirinta na makamashin nukliya ba.
Tun kafin ya sake dawowa kan kujerar shugabancin kasar Amurka, a karo na biyu, shugaban yake barzanar zai tursaswa iran ta amince don tattaunawa da ita kan shirinta na makamashin nukliya.
Amma idan ta ki amincewa zai yi amfani da karfin don wargaza shirinta na makamshin nukliya don ba zata amince iran ta mallaka makaman Nukliya ba.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: a wannan atisayen sojojin ruwa na yankin da kuma kara da cewa
এছাড়াও পড়ুন:
Iran da china Za su Yi Bikcin Cika Shekaru 55 Da Huldar Diplomasiya Tsakaninsu
Adai dai lokacin da bikin cika shekaru 55 na kulla hulda diplomsiya tsakanin Iran da China ke kara karatowa ta , dukkan kasashen biyu suna kokarin ganin sun kara karfafa alakar dake tsakaninsu , Ambasado Ahmad Fazli ya jaddada game da muhimmancin karfafa dangantaka a mataki na kasa da kasa, bisa hangen nesa da girmama juna.
Ganawar da aka yi tsakanin jakadan kasar iran a bejin Rahmani Fazli da Miao Deyu matakimakin ministan harkokin wajen kasar china ta nuna aniyar kasashen biyu na kara karfafa dangantakarsu ta dogon lokaci.
A lokacin ganawar da mataimakin ministan harkokin wajen kasar china rahmani ya jadda muhimmancin kara dankon zumunci tsakanin iran da china, musamman ma yin muhimmacin aiki tare a yankin, don haka bikin cika shekara 55 zai zama wata damace da zaa kara fadada dangantaka da yin aiki tare
Bangaren iran a shirye yake yayi aiki da kasar china don karfafa muamala da zurfafa yin aiki tare a bangarori daban daban bisa yarjejeniyar da shuwagabannin kasashen biyu suka cimma matsaya akai,
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Faransa: An Fara Shari’ar Shugaban ‘Yan Tawayen DRC Bisa Laifuna Akan Bil’adama November 13, 2025 Almayadin Ta Sami Rahoton Hukumar Makamashin Ta Duniya ( IEA) Aka Cewa Iran Tana Aiki Da Dukkanin Ka’idoji November 13, 2025 Janar Ali Fadwi: Muna Aiki Tukuru Domin Sabunta Nisan Makamanmu Masu Linzami November 13, 2025 Ministocin Harkokin Wajen Iran da Rasha sun Tattauna Gabanin Taron Gwamnonin IAEA November 13, 2025 Iraki: An Fara Sanar Da Sakamakon Farko Na Babban Zaben Da Aka Gudanar November 13, 2025 Kenya: An gano tarin zinari a karkashin kasa da darajarsa ta haura Dala biliyan 5 November 13, 2025 Gaza: Hamas Ta Nemi Kawo Karshen Kisan Kiyashi Da Lamunce Shigar Da Taimako November 13, 2025 MDD ta yi gargadi game da hadarin yunwa a wasu sassa na duniya November 13, 2025 Amurka Na Shirye-Shiryen Aikewa Da Sojoji Guda 1000 A Iyakar Isra’ila Da Yankin Gaza November 12, 2025 Shugaban Iran Ya Aike Da Wasika Ta Musamman Zuwa Ga Yarima Mai Jiran Gado Na Saudiyya November 12, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci