Isra’ila ta kaddamar da hare hare kan wasu gine-gine da cibiyoyi a sassa daban daban na Iran ciki har da Tehran babban birni a cikin daren jiya wayewar wannan safiya ta Juma’a.

Kafofin yada labarai na Iran sun ce akwai mata da yara da dama daga cikin wadanda suka yi shahada a hare-haren.

An kuma bayar da rahoton kai hari a wurare a Natanz, Khorramabad, da Khondab, da dai sauransu.

Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce harin da Isra’ila ta kai wa Iran zai kai tsawon kwanaki idab akwai bukatar hakan.

“Za a ci gaba da gudanar da wannan aiki na tsawon kwanaki kamar yadda ake tsara don kawar da wannan barazanar,” in ji Netanyahu a cikin wata sanarwa ta bidiyo.

Hare-haren da sojojin gwamnatin sahyoniyawan suka kai kan Tehran ya yi sanadiyar shahadar wasu fitattun masana kimiyyar nukiliya na Iran, Mohammad Mahdi Tehranchi da Fereydoon Abbasi, dama wasu fararen hula.

Tehranchi shi ne shugaban jami’ar Azad ta Musulunci ta Iran.

Fereydoon Abbasi ya kasance tsohon shugaban hukumar makamashin nukiliya ta Iran.

An dakatar da zirga-zirgar jiragai a filin jirgin saman Imam Khumaini na Tehran.

Harin ya zo ne kwanaki biyu gabanin wani sabon zagaye na shawarwarin nukiliyar Iran da Amurka.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin APC ta jefa ’yan Najeriya cikin ƙangin talauci — Shugabar LP

Muƙaddashiyar Shugabar Jam’iyyar LP, Sanata Nenadi Esther Usman, ta ce gwamnatin APC ce ta fi jefa ’yan Najeriya cikin talauci sama da kowace gwamnati a tarihin ƙasar nan.

Da ta ke zantawa da manema labarai a Jihar Kaduna, Sanatan ta ce jam’iyyar LP ta shirya tsaf don gyara kurakuran da gwamnatin APC ta tafka.

Gwamna Bauchi ya sasanta manoma da makiyaya a Darazo Ambaliya ta yi ajalin mutane, ta lalata gidaje a Adamawa

Ta roƙi ’yan Najeriya da su bai wa LP goyon baya, inda ta ce jam’iyyar za ta kawo canji na gaskiya.

Ta ce halin da ake ciki na wahala a ƙasar nan ya yi muni ƙwarai, kuma ta d6ora alhakin hakan kan gwamnatin APC.

Game da sauya sheƙa da wasu ’yan siyasa ke yi daga jam’iyyun adawa zuwa APC, ciki har da wasu daga LP, Sanatan ta bayyana hakan a matsayin abin takaici da rashin sanin darajar kai.

A cewarta, ba daidai ba ne mutum ya samu madafun iko da tallafin wata jam’iyya, amma daga baya ya koma wata jam’iyya don kawai samun riba ba.

Sai dai ta ce wannan ba zai girgiza jam’iyyarsu ba, domin ƙarfin jam’iyyar na ƙara bayyana da goyon bayan talakawan Najeriya.

Sanata Esther ta amince cewa jam’iyyar ta yi wasu kurakurai a baya, musamman wajen zaɓen ’yan takara da ba su dace da manufofin jam’iyyar ba.

Amma ta tabbatar da cewa sun ɗauki darasi, kuma suna shirin yin gyara kafin babban zaɓe na gaba.

“Yawancin waɗanda suka bar jam’iyyar ba su da cikakken ƙudirin kafa sabuwar Najeriya. Ficewarsu ta sa mun fi fahimtar juna kuma ta ƙara mana ƙarfi,” in ji ta.

Ta roƙi mambobin jam’iyyar da aka ɓata ws raj da su manta da saɓanin, su haɗa kai domin ƙarfafa jam’iyyar.

Ta ce ana shirin gudanar da zaɓen shugabanni a matakin ƙasa da kuma babban taron ƙasa kuma Majalisar Zartarwar Jam’iyyar (NEC) ta amince da waɗannan sauye-sauye da suke buƙata.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Pezeshkiya: Iran A Shirye Take Don Mu’amala Amma Bazata Bar Hakkinta Ba
  • Iran Ta Ce Amurka Ce Bayan Hare-haren Da Aka Kai Zahidan
  • Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyar Mutuwar Mutane Da Dama A Yola
  •  Rasha Ta Kai Munanan Hare-hare Akan Birnin Kiev Na Ukiraniya
  • Gwamnatin APC ta jefa ’yan Najeriya cikin ƙangin talauci — Shugabar LP
  • Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Yi Furuci Da Halakar Sojan Guda Da Ya Jikkata A Zirin Gaza
  • Za a ɗauke wuta na tsawon kwanaki 25 a Legas — TCN
  • Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50
  • ‘Yan Jarida Da Suka yi Shahada A Gaza Sun Kai 232, Yayin Da Wadanda Suka Rasa Rayukansu Sakamakon Yunwa Suka Kai 122