Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya
Published: 14th, June 2025 GMT
Babu abin da ya rage yanzu, illa babatun zantukan siyasa da ‘yan siyasar ke ta fama yi a kasar, wadanda suka jarabtu da matukar son mulki. Wannan abu da ke faruwa yanzu, ko shakka babu zai canja, zai canja din ne kuwa yayin da ‘yan siyasar ke aiwatar da tsare-tsarensu, sai masu jefa kuri’u a Nijeriya kuma su yanke hukunci.
A bisa dukkan alamu, jam’iyyar APC ta dukufa wajen kara habaka karfinta ne kawai da ganimar ‘yan adawa. Tana ta faman sa kanta cikin rigingimu, har wadanda ba su shafe ta ba a cikin shekaru biyun da ya rage mata ta yi gaba na kunci da tsanani. Maimakon gwamnatin ta mayar da hankali kan nauye-nauyen da ke kanta, na yi wa al’ummar kasa aiki; sai ta buge da yin fada da jam’iyyar adawa, kullum cikin wasa wukarta; a gefe guda kuma gazawar gwamnatin na fitowa fili.
Kura-kuren gwamnatin sun hada da; girman kai wajen tafiyar da al’amuranta, rashin tafiyar da abubuwa yadda ya kamata; tunanin cewa, jawo ‘yan adawa zai ba ta dama tare da karfin yin fada da kuma lashe zabe; ta hanyar zaben shugaban kasa cikin sauki, wanda kowane bangare zai bayar da gudunmawarsa. Amma, babbar matsalar ita ce; shugaban kasar ba shi da kima a kusan dukkanin sassan kasar.
Jam’iyya mai mulki, za ta iya bunkasa damar da take da ita, idan ba ta tsayar da Tinubu a 2027 ba, musamman idan za ta tsayar da matashi, lafiyayye, dan siyasa mai gaskiya da son ci gaba. Hakan kuwa, da alamu ba zai yiwu ba, domin Tinubu shi ne ked a wuka da nama a jam’iyyar.
Shugaban kasa da kansa, ba zai iya bayar da shawarar yadda za a yi gyara ta hanyar kawo wani dan takarar da ya dace ba. Idan Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu, zai kasance a matsayin dan takara, APC za ta yi amfani da dukkanin damammakin da take das u, musamman na amfani da kudi wajen sayen kuri’u da masu zabe. Rage Muslman Arewa saboda Kiristocin Arewa, na iya zama hadari, amma wannan shi ne kawai abin da za a iya yi.
Haka zalika, jam’iyyar ta zama dakikiyar daliba, domin babu abin da take karantawa illa yadda za ta samu damammaki iri daban-daban na siyasa kadai. Dandazon da ‘yan siyasa suka yi a cikinta, ba karamar barazana ba ce ga masu bukatu daban-daban, musamman idan aka kasa biya musu bukatunsu.
Ko shakka babu, Arewa za ta yi matukar tasiri a zaben da za a yi. Shi ne yankin day a fuskantar ayyukan ta’addanci da kuma mummunan talauci da ke biye da su har zuwa rumfunansu na zabe. Saboda haka, dole ne jam’iyyar ta yi aiki tukur don kaucewa sake faruwar zaben 2015, lokacin da jam’iyya mai mulki ta fuskanci daukacin yankin da suka yi mata zanga-zanga.
Kudu-maso-yamma, za su iya goyon bayansa idan ya kasance manyan ‘yan adawa sun fitar da wani dan takarar daga Arewa, amma wannan rashin kwanciyar hankali da ake fama das hi, ya kamata a ce ya hana kowa barci.
Tasirin Wike, zai iya raunanawa ko karfafawa; ya danganta da matakin da ‘yan adawa suka dauka game da rikice-rikice a Kudu-maso-kudu, wanda zai iya daidai da bukatunsu; ba abubuwan da suka dace ba. Za a lalata jam’iyyar LP ba tare da Obi ba, a kuma matse shi a matsayinsa na dan takararta.
Burin Obi yanzu, ya wuce batun jam’iyyar LP; amma akwai barazanar samun raguwa a matsayinsa na dan siyasa, idan ya yanke shawarar da za ta iya raba mabiyansa. Kudu-maso-gabas, sun kagu su ga sun samu mukamin shugabancin kasa, wanda hakan ke nuna kishinta na samun daidaito. Hakan, na iya yiwuwa ta hanyar samun daidaito, ana iya samun hakan ta hanyar yarjejeniya a tsakanin yankunan da ake da su.
Da alamu dai, tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar ne ke da babbar matsala. Ya yi rauni da yawa da zai iya ja da bukatar Tinubu na neman wa’adi na biyu. Don haka, sake barin jam’iyyar PDP tare da neman wata jam’iyyar daban, hanya ce kawai ta kasha makudan kudade da bata lokaci da sauran makamantansu.
PDP a halin yanzu, na zub da jini ne sakamakon zagon kasan da jam’iyya mai mulki ke yi mata. Babbar kadararta shi ne Atiku, amma kuma shi ne babbar matsalarta. Matsayinsa na farko a jam’iyyar, shi ne ke haifar da korafe-korafe da rudani, zai yi wuya PDP tare da Atiku su shiga yarjejeniyar da za ta bayar da dama a karo na biyu.
Idan da PDP za ta iya gyaruwa ta samu nasara a kan APC, dab a ta damu da neman biyan bukatun da suka fi muni ko kawo rudani ba. Jam’iyyar da ta taba yi wa al’ummar kasar barazana, yanzu kuma tana cikin sadar kafa tarihi wajen rubuta ta a matsayin wacce da fi bayar da gudunmawa wajen samun nasarar APC 2027.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: a jam iyyar
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai
A cewar Bawa, gwamnatocin da a karkashinsu aka wawashe dukiyar kasa, su ne na Mulkin Tsohon Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo (daga 1999 zuwa 2006), sai Marigayi Shugaba Umaru Musa Yar’Adua (daga 2007 zuwa 2009), kazalika a mulkin Shugaba Goodluck Jonathan daga (2010 zuwa 2014), sai kuma mulkin Muhammadu Buhari (daga 2015 zuwa 2023).
Wadannan bayanai na kunshe cikin littafin, ‘The Shadow Of Loot and Loss – Uncobering Nigeria’s Petrol Subsidy Fraud,’ wanda tsohon sarkin yaki da cin hanci da rashawa ya rubuta.
Alkaluman da Bawa ya bayyana daga cikin gwamnatocin hudu, shugaba Buhari ne ke kan gaba wajen biyan tallafin da ake ta cece-kuce akai na Naira tiriliyan 11, sai kuma na Jonathan wanda ya kashe Naira tiriliyan 3.9. Gwamnatin Obasanjo ta zo na uku da Naira biliyan 812 yayin da ‘Yar’aduwa ke biye da Naira biliyan 794.
Obasanjo da Buhari sun shafe shekaru takwas suna mulki yayin da Jonathan ya yi mulki na tsawon shekaru shida, tun da farko ya kammala shekaru biyu da gwamnatin Yar’adua ta bari, a matsayin mataimakin marigayin, inda ya lashe zaben shugaban kasa a shekarar 2011.
A cikin littafin mai shafuka 317, Bawa ya ce kudaden tallafin, wadanda galibi na yaudara ne, ana samun su ne ta hanyar rashin isassun tsare-tsare, raunin tsarin aiwatar da doka, da kuma rashin gaskiya a cikin dukkan tsarin.
Bawa ya ce wadannan kura-kurai sun karfafa karuwar kudaden tallafin daga Naira biliyan 123 a shekarar 2006 zuwa Naira biliyan 886 a shekarar 2014 da kuma mummunan adadi na Naira tiriliyan 11 a shekarar 2023.
Tsohon shugaban na EFCC ya ci gaba da cewa za’a iya bayyana badakalar tallafin man fetur ta Nijeriya ta hanyar amfani da triangle na zamba na “Tsarin (Needs), Opportunity and Rationalisation.”
Ya ce, “Matsi shi ne abin da zai sa mutum ya yi zamba, samun dama kuma ita ce ke bayar da yanayin da mutum zai aikata zambar.
Yadda Aka Aiwatar Da Badakalar
Bawa ya gano hauhawar farashin shigo da kayayyaki, da sauya lokacin daftarin kaya, rashin bayyana dawo da kayan da aka shigo da su ta sama da kasa, da jirgin ruwa mai yawo, shigo da kaya guda daya, tare da biyan tallafi a kansa sau biyu, na daga cikin hanyoyin da aka tafka badakalar tallafin man fetur.
A cewarsa, kamfanonin sayar da man sun yi amfani da yawan shigo da kayayyaki don kara yawan kudaden tallafi daga karshen shekarun 2010.
Ya ce binciken da aka gudanar ya sa hukumar EFCC ta gano haramtattun kudaden da suka haura Naira biliyan 30.
Bawa ya ci gaba da cewa, “A lokuta da dama, an samu jami’an gwamnati da saninsu ko kuma ba da saninsu ba, ta hanyar buga tambari da sanya hannu a cikin takardun jabun, wasu jami’an sun ce sun sanya hannu a kan takardun a lokacin da suke bakin aiki, duk da cewa suna sane da cewa lamarin ba haka yake ba, akwai wadanda suka sanya hannu kan takardun bogi, ba tare da sanin cewa an kirkiresu ba ne.
Ya ba da misali da yadda wani kamfani ya shigo da lita miliyan biyar kasa da mai fiye da lita miliyan 12. An biya kamfanin tallafin Naira miliyan 700, wanda bai cancanta ba.”
Wannan a cewarsa lamari ya ci gaba da haifar da tambayoyi masu mahimmanci game da hanyoyin damfara, gazawar sa ido na hukumomi, da kuma yadda EFCC ta gano wadannan haramtattun ayyuka.
Hanyar Kawo Karshen Lamarin
Dangane da kokarin hukumar na duba matsalar, Bawa ya ba da tarihin bincike, kamawa, tuhume-tuhume, yanke hukunci da kwato haramtattun dukiyoyi da hukumar ta yi.
Ya ce duk da cewa ba a samu wasu laifuka ba a shekarar 2006 da 2007, hukumar ta kwato Naira biliyan 11.5 a shekarar 2008, Naira biliyan 4.88 a shekarar 2009, da kuma Naira biliyan 10.3 a shekarar 2010.
Tsohon shugaban hukumar ta EFCC ya bayyana wata badakala da aka yi a 2011 ta tallafin man fetur, “a lokacin ne muka gano wasu haramtattum ayyukan da suka kai Naira biliyan 41.7.
“A dunkule, ayyukan damfara sun kai kusan Naira biliyan 68, wanda kusan kashi 80 cikin 100 an kwato su,” in ji shi.
Bawa ya kara da cewa, a cikin shekaru 25 na mulkin dimokuradiyya, Nijeriya ta kashe Naira tiriliyan 16.5 wajen bayar da tallafi, inda ya kara da cewa abin da ke daure kai ga daukacin al’amura shi ne yadda aka kashe kaso daga cikin kudaden wajen yin ikirarin karya da satar dukiyar kasa.
Hanyar Samun Ci Gaba
Bawa ya yi nuni da cewa, shi tallafin a kansa ba wani sharri ba ne; amma duk da haka, aiwatar da aikinta na yaudara ya sa gwamnati ta ki amincewa da dimbin albarkatun da aka tanada domin samar da ababen more rayuwa, inganta harkokin ilimi da kiwon lafiya, wadanda ke amfanar da marasa galihu a Nijeriya.
Don haka ya yi kira da a samar da ingantaccen tsarin bayar da tallafi.
Ya ce, “Kiyaye tsarin tallafin da aka sarrafa da kyau zai iya ba da agajin da ake bukata ga masu rauni ta hanyar tabbatar da cewa an dakatar da tsadar rayuwa, sannan gwamnatin ta tsaya tsayin daka wajen samar da wani abin dogaro ga matsalolin tattalin arziki.
“Wannan yana jaddada muhimmancin samar da ingantattun hanyoyin sa ido da daidaita yadda ake raba tallafin don hana cin zarafi da tabbatar da sun cika manufarsu.”
Bawa ya kuma yi kira da a ji tsoron Allah da gaske da kuma samar da ingantaccen tsarin adalci.
Bawa ya ce, “Tsarin ba wai kawai kayan ya ke ba wa kariya da kuma dakile laifuka ba, har ma ya mallakar karfin bincike da kuma hukunta laifukan da suka dace, yana da matukar muhimmanci, irin wannan tsarin na samar da amana da amincewa a tsakanin ‘yan kasa, tare da karfafa hadin gwiwar jama’a da kuma tabbatar da doka da oda.”
Tsohon shugaban na EFCC ya bukaci ‘yan Nijeriya da na kasashen waje da su canja halayensu, su bi ka’idojin da’a, su sanya al’ummar kasa a zuciyarsu sama da kansu.
Bugu da kari, ya yi kira da a samar da isassun kudade tare da tura fasahar kere-kere a cibiyoyin gwamnati domin dakile cin hanci da rashawa.
“Su koma al’adar yin abin da ya dace, ba tare da la’akari da yanayin ba, hakan na iya haifar da sauye-sauye masu dorewa a cikin al’amuran al’umma,” in ji shi.
LEADERSHIP Sunday ta ruwaito cewa an samu wasu ‘yan Nijeriya da dama da laifin zamba a cikin tallafin man fetur, na baya-bayan nan shi ne Mamman Ali, dan Ahmadu Ali, tsohon shugaban jam’iyyar PDP mai mulki a lokacin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp