Wakilin dindindin na kasar Sin a hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya ko IAEA Li Song, ya ce kasarsa na matukar Allah wadai da harin Isra’ila kan cibiyoyin sarrafa nukiliyar Iran da ake amfani da su domin ayyukan zaman lafiya.

Li Song, ya bayyana hakan ne a jiya Juma’a, yayin taron manyan jami’an majalisar gudanarwar hukumar ta IAEA, game da batun hare-haren da Isra’ila ta kaddamar kan cibiyoyin sarrafa nukiliyar Iran.

Ya ce, har kullum Sin na mayar da hankali ga zakulo matakan wanzar da zaman lafiya, dangane da batun nukiliyar Iran ta hanyoyin siyasa da diflomasiyya, tana kuma adawa da kakaba takunkumai ba bisa ka’ida ba daga bangare guda. Har ila yau, Sin za ta ci gaba da tattaunawa ta kut-da-kut da dukkanin sassan da batun ya shafa, tare da shawo kan batutuwan gaggawa dake gaban majalisar gudanarwar hukumar ta IAEA. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Rundinar IRGC, ta sanar da shahadar babban kwamandanta Manjo Janar Hossein Salami a harin ta’addancin Isra’ila

Dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran sun sanar a cikin wani sako mai cike da alhini da shahadar Manjo Janar Hossein Salami, babban kwamandan dakarun IRGC wanda ya yi shahada da asubahin ranar Juma’ar nan yayin wani hari na ta’addanci” da gwamnatin sahyoniyawan ta kai kan hedkwatar rundunar.

Hukumar soji tana jinjinawa wannan babban kwamandan da aka gabatar a matsayin babban jigo wajen kare manufofin juyin juya halin Musulunci na Iran, tare da yin alkawarin mayar da martani mai tsauri ga makiya.

Ga yadda sanarwar IRGC ta kasance :

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai

A cikin bakin ciki da radadi muna sanar da shahadar Manjo Janar Hossein Salami, babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci, da da wasu mukarabansa, a lokacin harin ta’addancin da gwamnatin sahayoniya ta kai a safiyar wannan ranar ta Juma’a akan hedkwatar IRGC yayin da suke gudanar da muhimmin aiki na tsaron kasa.

Muna mika ta’aziyyarmu ga Jagoran juyin juya halin Musulunci kuma babban kwamandan sojojin kasar, Imam Khamenei, da iyalan duk wadanda abun ya shafa.

 Duk da wannan harin na dabbanci, muna tabbatar wa al’ummar Iran masu daraja cewa, har yanzu rundunar sojojin Iran a shirye suke don maida martani ga gwamnatin sahyoniyawan.

Nan ba da jimawa ba za a isar da cikakken bayani kan halin da ake ciki biyo bayan harin na makiya da kuma matakin da za a dauka na hukunta su.

Haka zalika kafofin yada labarai na Iran sun rawaito shahadar babban hafsan hafsoshin sojojin kasar Iran Manjo Janar Mohammad Hossein Baqeri.

Shi ma Manjo Janar Baqeri ya yi shahada a wani harin ta’addanci da gwamnatin sahyoniya ta kai birnin Tehran a safiyar yau Juma’a.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai
  • Gwamnatin Najeriya Ta Yi Allawadai Da Harin Da “Isra’ila” Ta Kawo Wa Iran
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • Harin Isra’ila a kan Iran ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zama dar-dar
  • Sakon Jagora : Isra’ila ta jira hukunci mai tsanani bayan hari kan Iran
  • Rundinar IRGC, ta sanar da shahadar babban kwamandanta Manjo Janar Hossein Salami a harin ta’addancin Isra’ila
  • Iran ta caccaki kudurin IAEA wanda ta ce yana cike da siyasa