Leadership News Hausa:
2025-07-30@21:57:47 GMT

Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su

Published: 14th, June 2025 GMT

Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su

Ciwon Olsa

Ga mai fama da ciwon Olsa, sai ya nemi garin ‘ya’yan Gwanda cokalin shayi daya; ya zuba a kunu sau daya a rana, har tsawon kwana bakwai, za a rabu da ita da yardar Allah.

 

Ruwan Maniyyi

Ga masu fama da karancin ruwan maniyyi, sai ya nemi garin ‘ya’yan Gwanda da Madara ya hada ya rika sha, wannan hadi na matukar kara ruwan maniyyi.

Ciwon Siga: Shan garin ‘ya’yan danyar Gwanda cokali daya a ruwan dumi, na sauke Siga cikin kankanin lokaci a jikin mutum da izinin Allah.

 

Hana Daukar Ciki

Ga masu son yin tsarin iyali, shan garin ‘ya’yan Gwanda cokalin shayi daya a ruwan dumi bayan yin jima’i, na hana ciki ya shiga.

 

Taifot Da Maleriya

Ana kiba ‘ya’yan Gwanda a tace a ruwa, kimanin lita hudu (Galan daya), a zuba zuma kimanin cokali 10 a sha rabin kofi sau biyu a rana har ya kare, za a samu lafiya in sha Allah.

 

Cutar Daji (Cancer)

Shan ruwan ‘ya’yan Gwanda da aka kirba aka tace kofi daya a rana sau daya, yana rigakafin kamuwa da ciwon Daji.

Amma fa ban da masu jinjirin ciki ko kuma wadanda ba su da daya daga cikin wadannan cutuka. Sannan, har masu ciwon Hanta ma za su iya yin amfani da shi in sha Allah.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: ya yan Gwanda

এছাড়াও পড়ুন:

Mamakon ruwan sama ya haddasa ambaliya a Maiduguri 

Ruwan sama mai ƙarfi da ya sauka da safiyar ranar Laraba a Maiduguri, Babban Birnin Jihar Borno, ya haddasa ambaliya.

Ruwan wanda ya fara sauka tun da misalin ƙarfe 5 na Asuba, ya cika tituna da gidaje musamman a unguwannin Dala, Bulunkutu, titin Damboa, filin Polo, da Federal Low Cost.

Sojoji sun daƙile hari, sun kashe mayaƙan Boko Haram 9 a Borno Shugaban hukumar zabe ta jihar Bauchi ya rasu

Ambaliyar ta haifar da cikas a rayuwar jama’a, inda ruwa ya lalata dukiyoyi mutane masu tarin yawa.

Mutane da dama dun fice daga gidajensu domin neman mafaka, musamman waɗanda gidajensu ruwa ya mamaye.

Hakazalika, wasu tituna sun shafe sakamakon mamakon ruwan, lamarin da ya hana mutane fita ko komawa gidajensu da kuma yin ayyukansu na yau da kullum.

Wasu daga cikin mazauna garin sun ce ambaliyar ta tsananta ne saboda magudanan ruwa sun cika da shara irin su robobi, datti da tarkacen kayan gini.

Hakan ya hana ruwa tafiya yadda ya kamata.

Wani da ya nemi a ɓoye sunansa ya ce mafi yawan magudanan ruwan Maiduguri ba sa aiki yadda ya kamata saboda sun toshe da shara.

Ya ƙara da cewa rashin kula da tsaftar muhalli ne ya haddasa irin wannan matsala.

A halin yanzu, akwai buƙatar gwamnati ta ƙara sanya ido, ta tsaurara dokokin muhalli, da kuma wayar da kan jama’a kan muhimmancin tsaftar gari.

Har ila yau, akwai buƙatar a gyara magudanan ruwa domin gujewa irin wannan ambaliya a nan gaba.

Masana sun gargaɗi jama’a cewa ana sa ran samum mamakon ruwan sama a makonni masu zuwa.

Amma an buƙaci jama’a su ɗauki matakan kariya da kuma haɗa kai da hukumomi domin shawo kan lamarin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mamakon ruwan sama ya haddasa ambaliya a Maiduguri 
  • Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana
  • Yadda ’yan bindiga suka tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina
  • APC Zamfara Ta Taya Sabon Sarkin Katsinar Gusau Murna
  • An shawarci Manoman Kwara Da Su Yi Taka-Tsan-Tsan Saboda Hasashen Ruwa Da Tsawa A Jihar
  • ’Yan bindiga sun tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina
  • Mutum daya Yayi Shahada 4 Sun Ji Rauna Sanadiyar Hare-Haren HKI A Lebanon
  • Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara
  • Gwamna Namadi Ya Biya Sama Da Naira Biliyan Daya Ga Tsofaffin Ma’aikata
  • Sin Ta Samar Da Manyan Manhajojin AI Sama Da 1500