Iran, ta yi wa Isra’ila ruwan makamai masu linzami
Published: 14th, June 2025 GMT
Iran ta kaddamar da wasu jerin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila a matsayin maida martani kan haren haren da Isra’ila ta kai wa kasar a cikin daren ranar Juma’a.
Bayanai sun ce hare-haren na Iran sun lalata gine-gine da dama da jikkata mutane yayin da wasu rahotannin ke cewa an samu hasarar rayuka na akalla mutum biyu.
A cewar rahotannin kafofin yada labaran Isra’ila daban-daban, makamai masu linzami na iran sun fada a yankunan Tel Aviv, Haifa, Beersheba da wasu wurare.
An bayar da rahoton barna mafi muni a birnin Tel Aviv, inda akalla makami mai linzami guda ya afkawa wani bene mai hawa 50, lamarin da ya janyo fashewar wani abu mai karfi wanda ya sa hayaki ya tashi a sararin samaniyar birnin.
A cewar darektan cibiyar nazarin dabarun da huldar kasa da kasa, Amir Al-Mousawi, daya daga cikin makami mai linzamin na Iran ya afkawa wata cibiyar binciken nukiliya da ke birnin Tel Aviv.
Wasu rahotanni sun ce an kuma yi nasarar kaiwa ma’aikatar harkokin sojan Isra’ila hari.
Gwamnatin kasar ta sanya takunkumi, inda ta umarci mazauna yankin da kada su buga hotuna ko bidiyo na wuraren da makami mai linzami na Iran ya kai hari, kamar yadda kafar yada labaran Isra’ila ta bayyana.
Birgediya Janar Ahmad Vahidi, da yake magana da gidan talabijin na iran, ya ce martanin na iran mai lakabin Operation True Promise III “zai ci gaba muddin akwai bukatar hakan,” yayin da ya sha alwashin daukar fansar jinin shahidai.
Tun da farko, Vahidi ya ce an kai hari a kalla wurare 150 a harin ramuwar gayya kan gwamnatin Isra’ila, ciki har da wasu sansanonin soji masu matukar muhimmanci.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu da ke da alaƙa da Wike
Rikici a babbar jam’iyyar adawa ta PDP, na ƙara ƙamari, bayan da jam’iyyar ta dakatar da sakatarenta na ƙasa, Sanata Samuel Anyanwu, da wasu da ake ganin ’yan tsagin Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike ne.
Mai magana da yawun jam’iyyar na ƙasa, Debo Ologunagba ne, ya sanar da dakatarwar bayan wani taro da Kwamitin Ayyuka na Ƙasa (NWC), ya gudanar a hedikwatar jam’iyyar da ke Abuja.
Zargin Kisan Kiristoci: Maganar Trump a kan Najeriya tsagwaron ƙarya ce — Shehu Sani Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia ta yi tazarce da kashi 97 an ƙuri’uSauran da aka dakatar sun haɗa da Mai Bai wa jam’iyyar Shawara kan Harkokin Shari’a, Kamaldeen Ajibade (SAN); Sakataren Tsara Harkokin Jam’iyya, Umar Bature; da Mataimakin Mai Bai wa jam’iyyar Shawara kan Harkokin Shari’a.
Rahotanni sun bayyana cewa waɗanda aka dakatar ba sa halartar tarukan jam’iyyar.
An dakatar da su na tsawon wata ɗaya, sannan aka miƙa lamarinsu ga Kwamitin Ladabtarwa na jam’iyyar PDP domin gudanar da bincike.
Waɗanda aka dakatar ’yan tsagin Wike ne, kuma sun raba ƙafa a rikicin da jam’iyyar ke fuskanta tun bayan zaɓen 2023.
Idan ba a manta ba, a ranar Juma’a ne, wata Babbar Kotu a Babban Birnin Tarayya, ta dakatar da PDP daga shirin gudanar da babban taronta da aka tsara yi a Ibadan, Jihar Oyo, a ranar 15 da 16 ga watan Nuwamba, 2025.
Sai dai jam’iyyar ta ce za ta ɗaukaka ƙara kan hukuncin, kuma hakan ba zai hana ta ci gaba da shirye-shiryen gudanar da taron ba.
Wasu daga cikin ’ya’yan jam’iyyar sun ce rashin jituwa a PDO shi ne babban dalilin da ya sa aka kai ƙarar taron’ kotu.