Uganda Ta Aike Da Sojoji Zuwa Sudan Ta Kudun Domin Kare Babban Birnin Kasar
Published: 11th, March 2025 GMT
Kasar Uganda ta sanar da aikewa da sojojinta zuwa birnin birnin kasar Sudan Ta Kudu, Juba saboda ba shi kariya. Sai dai har yanzu gwamnatin Sudan din ba ta tabbatar da hakan ba.
Babban hafsan hafsoshin sojojin kasar Uganda Janar Muhoozi Kainerugaba ya bayyana cewa; Rundunar musamman ta Ugandan ta shiga cikin birnin Juba, domin ba shi kariya.
Janar Muhoozi Kainerugaba ya kuma ce: “ Za mu kare dukkanin kasar Sudan Ta Kudu, kamar yadda za mu kare kasarmu. A wurinmu Salva Kiir ne mu ka aminta da cewa halartaccen shugaban kasar Sudan Ta Kudu,don haka duk wanda zai shelanta yaki akansa, ya shelanta yaki ne akan Uganda.”
Har ila yau janar din na Uganda ya kuma ce; “ Wadanda su ka aikata laifuka za su dandana kudarsu.”
A cikin kwanakin bayan nan an shiga dambaruwar siyasa a kasar Sudan Ta Kudu bayan da gwamnatin shugaban Salva Kiir ta kama jami’an soja da kuma na siyasa masu alaka da mataimakin shugaban kasar Reik Machar. Hakan ya biyo bayan barkewar wani sabon bore ne na ‘yan kabilar Nuer da su ka yi fada da sojojin gwamnati.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Sudan
এছাড়াও পড়ুন:
Shugabannin Sin Sun Yi Taron Koli Na Tattauna Aikin Raya Tattalin Arziki Don Tsara Abubuwan Da Za A Aiwatar A 2026
Mahukuntan kasar Sin sun gudanar da taron koli, na tattauna aikin raya tattalin arzikin kasar, don tsara abubuwan da za a aiwatar a shekarar 2026 dake tafe. An gudanar da taron ne a jiya Laraba da yau Alhamis, inda shugabannin kasar suka tantance abubuwa mafiya muhimmanci, wadanda za a aiwatar, dangane da raya tattalin arzikin kasar a shekara mai kamawa.
Cikin muhimmin jawabi da ya gabatar yayin taron, shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya waiwayi aikin raya tattalin arziki da Sin ta aiwatar a shekarar nan ta 2025, tare da fayyace halin da tattalin arzikin kasar ke ciki, da ma aikin da aka tsara gudanarwa a shekara mai zuwa.
Yayin taron, an yi amannar cewa shekarar 2025 ta fita daban, kuma za a kai ga cimma nasarar muradun raya tattalin arziki, da zamantakewar al’ummar kasar Sin na shekarar ta bana.
ADVERTISEMENTTaron ya kuma tabbatar da cewa, aikin raya tattalin arzikin Sin na shekara mai zuwa, zai karkata ne ga ayyuka irinsu bunkasa sayayya a cikin gida, da ci gaba wanda kirkire-kirkire ke ingizawa, da kara bude kofar kasar Sin ga sassan waje, da cikakken salon sauyi zuwa ci gaba marar dumama yanayi, da kyautata rayuwar al’umma. (Mai fassara: Saminu Alhassan)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA