HausaTv:
2025-12-14@16:47:03 GMT

 Uganda Ta Aike Da Sojoji Zuwa Sudan Ta Kudun Domin Kare Babban Birnin Kasar

Published: 11th, March 2025 GMT

Kasar Uganda ta sanar da aikewa da sojojinta zuwa birnin birnin kasar Sudan Ta Kudu, Juba saboda ba shi kariya. Sai dai har yanzu gwamnatin Sudan din ba ta  tabbatar da hakan ba.

 Babban hafsan hafsoshin sojojin kasar Uganda Janar Muhoozi Kainerugaba ya bayyana cewa; Rundunar musamman ta Ugandan ta shiga cikin birnin Juba, domin ba shi kariya.

Janar Muhoozi Kainerugaba ya kuma ce: “ Za mu kare dukkanin kasar Sudan  Ta Kudu, kamar yadda za mu kare kasarmu. A wurinmu Salva Kiir ne mu ka aminta da cewa halartaccen shugaban kasar Sudan  Ta Kudu,don haka duk wanda zai shelanta yaki akansa, ya shelanta yaki ne akan Uganda.”

Har ila yau janar din na Uganda ya kuma ce; “  Wadanda su ka aikata laifuka za su dandana kudarsu.”

A cikin kwanakin bayan nan an shiga dambaruwar siyasa a kasar Sudan Ta Kudu bayan da gwamnatin shugaban Salva Kiir ta kama jami’an soja da kuma na siyasa masu alaka da mataimakin shugaban kasar Reik Machar. Hakan ya biyo bayan barkewar wani sabon bore ne na ‘yan kabilar Nuer da su ka yi fada da sojojin gwamnati.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Sudan

এছাড়াও পড়ুন:

Tsohon Jakadan Singapore A MDD Ya Jinjinawa Hangen Nesan Kasar Sin

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Samar Da Damammakin Raya Tattalin Arziki Ga Duniya A Shekara Mai Zuwa December 13, 2025 Daga Birnin Sin Sin Ta Gudanar Da Taron Tunawa Da Kisan Kiyashin Nanjing December 13, 2025 Daga Birnin Sin Kakakin Rasha: Kisan Kiyashin Nanjing Ya Nuna Zaluncin Ra’ayin Nuna Karfin Soja Na Japan December 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Yi Kira Da A Gaggauta Tsagaita Bude Wuta A Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo 
  • Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Samar Da Damammakin Raya Tattalin Arziki Ga Duniya A Shekara Mai Zuwa
  • Tsohon Jakadan Singapore A MDD Ya Jinjinawa Hangen Nesan Kasar Sin
  • Sin Ta Gudanar Da Taron Tunawa Da Kisan Kiyashin Nanjing
  • Bankin Ajiya na Jihar Jigawa Ya Karamar Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu
  • Majalisar Dinkin Duniya Za ta Yi Zama Da Bangarorin Da ke Yaki A Sudan
  • Duniyarmu A Yau: Iran Da Amurka A Yakin Kwanaki 12 Wa Ya Sami Nasara
  • Yadda Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samar Da Karin Damammaki Ga Kasashe Masu Tasowa
  •  Turkiya A Shirye Take Ta Aike Da Sojoji Zuwa Yankin Gaza
  • Hukumomin Ilimi a Jihar Jigawa Sun Kare Kasafin Kudinsu a Gaban Majalisa