HausaTv:
2025-07-30@15:32:00 GMT

IRGC : Iran ta kai hare hare wurare a kalla 150 a Isra’ila

Published: 14th, June 2025 GMT

Wani babban jami’in sojan Iran ya ce an kai hare-hare a kalla wurare 150 a farmakin ramuwar gayya kan gwamnatin Isra’ila, ciki har da wasu sansanonin soji masu matukar muhimmanci.

Da yake zantawa da gidan talabijin na kasar da sanyin safiyar Asabar, Birgediya Janar Ahmad Vahidi, babban mai ba da shawara ga babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran ya ce, rundunar ta IRGC ta yi nasarar aiwatar da shirinta na Operation True Promise III.

A cewar kwamandan na IRGC, an kuma kai hari kan ma’aikatar harkokin soji da cibiyoyin soji da masana’antu a lokacin da Jamhuriyar Musulunci ta Iran ke daukar fansa.

Daga cikin wadanda harin ya rutsa da su sun hada da Manjo Janar Mohammad Bagheri, babban hafsan hafsoshin sojojin Iran, Birgediya Janar Amir Ali Hajizadeh, shugaban sashin kula da sararin samaniyar IRGC, da Manjo Janar Gholam-Ali Rashid, kwamandan babban shalkwatar Khatam al-Anbiya ta kasar.

Har ila yau, hare-haren sun yi sanadin mutuwar tsoffin masana kimiyyar nukiliya Mohammad-Mehdi Tehranchi, Fereydoun Abbasi, da Dr. Abdol-Hamid Minoucher, tare da fararen hula fiye da 70 da suka hada da yara da mata.

Duk da haka, ya sake nanata cewa wannan babban “kuskure” ne daga bangaren Isra’ila, yana mai gargadin cewa, “Dole ne su jira sakamakon.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An fara shigar da kayan agaji a Gaza

An fara shigar da kayyakin agaji zuwa Zirin Gaza wadanda galibi ta sararin samaniya aka rika jefawa da jirage daga kasashen Jordan da Hadaddiyar Daular Larabawa.

Arshiyan Kohen, kakakin ma’aikatar tsaron Isra’ila ya ce, za a dakatar da farmakin soji na tsawon sa’o’i 10 a kowace rana a wasu sassan Gaza tare da ba da damar samun sabbin hanyoyin ba da agaji.

DW ya ruwaito cewa ana ci gaba danka kayayyakin tallafin a hannun kungiyoyin agaji na kasa da kasa da suke ci gaba da ayyukan rarrabasu.

Tinubu ya bai wa ’yan ƙwallon Nijeriya mata kyautar kuɗi da gida da lambar yabo An kashe ’yan ta’adda 45 a Neja

Sakataren Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Gutteress ya siffanta wannan matakin da mai sanyaya zuciya bayan damuwa da bala’in da mazauna Gaza suka tsinci kansu a ciki, yana mai fatar gaggauta shigar da kayayyakin agajin da kuma dorewarsa.

A yayin taron tattaunawa kan matsalolin da suke shafar ayyukan samar da abinci a Afrika ne Guterres ya faɗi  cewa yunwa ba za ta taɓa zama makamin da za a yi amfani da ita wajen yaƙi a duniya ba.

Babban jami’in bayar da agajin gaggawa na Majalisar Dinkin Duniya, Tom Fletcher ya yi maraba da matakin, yana mai cewa yanzu haka yana tuntubar kungiyoyi wadanda za su yi duk mai yiwuwa don isa ga mutane da dama da ke fama da yunwa a wannan lokaci.

Tuni dai kungiyoyin agaji suka gabatar da wasu korafe-korafe tun ba a yi nisa ba, don yi wa tufkar hanci muddin ana son kwalliya ta biya kudin sabulu a ayyukan agajin da aka fara bayan fiye da watanni uku da dakatar da su.

Ahmad Nadir, na kungiyar lafiya ta duniya WHO, ya ce tsame hannun Isra’ila daga batun karba da rabon kayan agaji ne kadai zai bai wa kwarraru kan ayyukan agaji damar gudanar da ayyukan da za a samu nasara.

A bayan nan ne Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya WFP ta ce kashi uku na al’ummar Gaza ba su ci abinci na kwanaki ba, kuma mutane 470,000 suna cikin yanayi na juriyar tsananin yunwa wanda tuni ya kai ga mutuwar wasu.

Isra’ila dai na ci gaba da fuskantar suka daga kasashen duniya, kan amfani da yunwa a matsayin makamin yaki kan al’ummar Falasdinu, lamarin da gwamnatin kasar ta ki amincewa da shi.

Akwai yunwa ta gaske a Gaza —Trump

Ko a wannan ɗin Litinin Shugaban Amurka Donald Trump ya ce “akwai yunwa ta gaske” a Gaza.

Shugaban na Amurka ya faɗi hakan ne bayan Firaiministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya nace kan cewa babu yunwa a yankin.

Da aka tambaye shi ko ya yarda da abin da Netanyahu ya fada cewar “ƙarya ce tsagwaronta” idan aka ce Isra’ila na ta’azzara yunwa a Gaza, shugaban na Amurka ya ce: “Ban sani ba…amma yaran nan da ka gan su, suna cikin yunwa…wannan yunwa ce ta gaske.”

Kalaman Trump na zuwa ne bayan shugaban hukumar kai agaji ta Majalisar Dinkin Duniya ya ce ana buƙatar abinci mai “ɗimbin yawa” domin magance halin yunwa da yankin ke ciki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwamandan NDA Ya Bukaci Dalibai Su Dage da Karatu a Taron FGC Malali
  • Gwamna Namadi Ya Naɗa Shugabannin Hukumar Hisbah Ta Jihar Jigawa
  • Manjo Janar Musawi: Ko Kadan Ba Mu Yarda Da Amurka Ba
  • An fara shigar da kayan agaji a Gaza
  • Iran Ta Ce Amurka Ce Bayan Hare-haren Da Aka Kai Zahidan
  • Ministan Yaɗa Labarai Ya Yi Jimamin Rasuwar Babban Ɗan Jarida Leon Usigbe
  •  Rasha Ta Kai Munanan Hare-hare Akan Birnin Kiev Na Ukiraniya
  • An Kwashe Duk Dabbobin Tsohon Akanta-Janar
  • Babban Jami’in Hamas A Gaza; Makiya ‘Yan Sahayoniyya Suna Rufe Gazawar Sojojinsu Da Kisan Kare Dangi
  • IRGC Ta Ja Kunnen Kasashen Turai Dangane Da Taimakon Da Suke Bawa HKI