Iran Kakkabo Wani Jirgin Yakin HKI Samfurin F-35 Karo Na 3 Tare Da Kama Matukinsa
Published: 14th, June 2025 GMT
Na’urorin kakkabo jiragen sama na Iran sun kakkabo jirgin sama na HKI samfurin F-35 a yammacin kasar, wanda shi ne karo na uku a cikin sa’oi 24.
Kamfanin dillancin labarun Tasnim ya nakalto majiyar tsaro na cewa; dakarun kare samaniyar jamhuriyar musulunci sun harbo jirgin sama samfurin F-35,kuma matukinsa ya fito ta hanyar amfani da lemar ceto.
Bayan wani lokaci daga faduwar jrigin da kuma fitowar matukinsa daga ciki, sojojin kasa na jamhuriyar musulunci ta Iran sun kama shi.
A jiya Juma’a ma dai daakrun kare sararin samaniyar jamhuriyar musulunci ta Iran, sun kakkabo jiragen saman na ‘yan sahayoniya wadanda kirar Amurka ne, kuma daya daga cikin jiragen yakin da take alfahari da su.
Shi dai jirgin yakin na Amurka samfurin F-35 yana da layar zana, kuma da wuya na’urar hangen nesa-Radar- ta iya tsinkayo shi. Kudin kowane daya daga cikin wadannan jiragen shi ne dalar Amurka miliyan 100.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Araqchi: Iran Zata Mayar Da Martanin Da Ba Zai Yiwu A Boye Ba Kan Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kanta
Ministan harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Idan aka maimaita ta’asar kai hari kan Iran, za ta mayar da martani ta hanyar da ba za a iya boyewa ba
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya mayar da martani kan barazanar da jami’an Amurka suka yi a baya-bayan nan, inda ya ce idan aka sake kai hari kan Iran, za ta mayar da martani mai tsauri wanda ba zai yiwu a iya boye ba.
Araghchi ya kara da cewa a cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter a ranar Litinin din nan cewa: Iran, kasar da ke da al’adun gargajiyar da ta shafe shekaru dubu bakwai na wayewar kai, ba za ta taba mika kai ga barazana da tsoratarwa ba. Iraniyawa ba su taba mika kai ga kasashen waje ba kuma ba su bukatar komai sai girmamawa.
Ya ci gaba da cewa: “Iran ta san hakikanin abin da aka yi mata da kuma abin da makiya suka fuskanta a lokacin farmakin da ‘yan sahayoniyya da Amurka suka yi a baya-bayan nan, ciki har da yawan munanan hare-haren da ta kai a matsayin daukan fansa wadanda ake ci gaba da boyewa. Don haka idan makiya suka sake kuskuren kai hari kan Iran, babu shakka zasu fuskanci martani mai gauni da ba zai yiwu a iya boyewa ba.