Hukumar Lamuni Ta Duniya IMF Da Bankin Duniya Sun Ce Bazasu Taimakawa Lebanon Ba Sai Da Sharudda
Published: 28th, February 2025 GMT
Hukumar bada lamuni ta Duniya IMF da kuma bankin duniya, manya-manyan cibiyoyin kudade a duniya sun ce ba zasu bada kudade don sake gina kasar Lebanon ba, sai sun cika wasu sharudda zuwa wani lokaci. Kuma sune samar da huldar jakadanci da HKI da kuma kwance damarar kungiyar Hizbullah.
Jaridar Al-Akhbar ta kasar Lebanon ta nakalto shugaban hukumar IMF Kristalina Georgieva ta fadawa gwamnan babban bankin kasar Lebanon na riko, Wassim Mansouri a wata haduwa da suka y ikan cewa kasarsa zata sami kudaden sake gidan kasar dag wajenta ne, tare da sharudda.
Rahoton ya kara da cewa kasashen Lebanon da Siriya zasu sami kudade daga cibiyoyin biyu ne kawaii dan sun samar da dangantakar diblomasiyya da HKI. Sannan kasar Lebanon kuma sai ta hada da kwance damara, ko ta kwace makaman kungiyar Hizbullah ta kasar wacce take yakar HKI.
Kafin haka dai ministan kudi na kasar Lebanon Yassin Jabir yace bankin duniya ta warewa kasar Lebanon dalar Amurka billiyon daya don sake gina kasar Lebanon bayan yakin da kungiyar Hizbulla ta fafata da HKI.
Labarin ya kammala da cewa idan kasar Lebanon ta cika sharuddan da kasashen yamma suka shardanta zata sami kudaden a cikin watan Maris mai zuwa.
Haka ma kungiyar tarayyar Turai tana da sharudda nab awa kasar Lebanon Euro miliyon E500 saboda ta taimaka ta hana bakin haure shiga kasashen turai daga kasar.
Wasu kafafen yada labarai a kasar Lebanon sun bayyana cewa kasar tana bukatar dalar Amurka biliyon biliyon 6-7 don sake gida abubuwan da HKI ta lalata a yankin da ta yi da kungiyar Hizbullah a shekara ta 2023-2024.
HKI ta amince da tsagaita wuta a dole bayan da mayakan hizbullah sun yi mata barna mai yawa a yakin.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: a kasar Lebanon
এছাড়াও পড়ুন:
Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawa guda bayan kwanaki 8
Kwanaki takwas bayan wata mummunar ambaliyar ruwa da ta mamaye garin Mokwa, hedikwatar Ƙaramar hukumar Mokwa a Jihar Neja, an gano gawar mutum ɗaya daga cikin waɗanda lamarin ya rutsa da su.
Mazauna garin sun shaida wa Daily Trust cewa, an tsinci gawar ne a ranar Alhamis a wata gona da ke kan hanyar wucewa kusa da wani wuri da aka fi sani da ‘dam’.
Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — FayemiA cewar shaidun gani da ido, an kasa tantance wanda abin ya shafa saboda gawar ta lalace. An binne shi ne a inda aka gano gawarsa.
Wata mazauniyar yankin mai suna Tswata Mai Rubutu da ta zanta da Aminiya ta wayar tarho, ta ce an tsinci gawar a kan hanyar da ruwa ke wucewa.
“Gawar wani babban mutum ne, amma ba za mu iya gane shi ba saboda tuni ya fara lalacewa. An binne shi a wurin tun da ba a iya motsa gawar,” in ji shi.
An yi ƙoƙarin jin ta bakin Darakta Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja, Abdullahi Baba Arah, domin ƙarin bayani lamarin ya ci tura.
Tun da farko hukumar ta tabbatar da mutuwar mutane 161, yayin da wasu da dama suka ɓace bayan iftila’in ambaliyar.