Hukumar bada lamuni ta Duniya IMF da kuma bankin duniya, manya-manyan cibiyoyin kudade a duniya sun ce ba zasu bada kudade don sake gina kasar Lebanon ba, sai sun cika wasu sharudda zuwa wani lokaci. Kuma sune samar da huldar jakadanci da HKI da kuma kwance damarar kungiyar Hizbullah.

Jaridar Al-Akhbar ta kasar Lebanon ta nakalto shugaban hukumar IMF Kristalina Georgieva ta fadawa gwamnan babban bankin kasar Lebanon na riko, Wassim Mansouri a wata haduwa da suka y ikan cewa kasarsa zata sami kudaden sake gidan kasar dag wajenta ne, tare da sharudda.

Rahoton ya kara da cewa kasashen Lebanon da Siriya zasu sami kudade daga cibiyoyin biyu ne kawaii dan sun samar da dangantakar diblomasiyya da HKI. Sannan kasar Lebanon kuma sai ta hada da kwance damara, ko ta kwace makaman kungiyar Hizbullah ta kasar wacce take yakar HKI.

Kafin haka dai ministan kudi na kasar Lebanon Yassin Jabir yace bankin duniya ta warewa kasar Lebanon dalar Amurka billiyon daya don sake gina kasar Lebanon bayan yakin da kungiyar Hizbulla ta fafata da HKI.

Labarin ya kammala da cewa idan kasar Lebanon ta cika sharuddan da kasashen yamma suka shardanta zata sami kudaden a cikin watan Maris mai zuwa.

Haka ma kungiyar tarayyar Turai tana da sharudda nab awa kasar Lebanon Euro miliyon E500 saboda ta taimaka ta hana bakin haure shiga kasashen turai daga kasar.

Wasu kafafen yada labarai a kasar Lebanon sun bayyana cewa kasar tana bukatar dalar Amurka biliyon biliyon 6-7 don sake gida abubuwan da HKI ta lalata a yankin da ta yi da kungiyar Hizbullah a shekara ta 2023-2024.

HKI ta amince da tsagaita wuta a dole bayan da mayakan hizbullah sun yi mata barna mai yawa a yakin.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: a kasar Lebanon

এছাড়াও পড়ুন:

Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya tare da kiyaye hadin kai

Shugaban kasar Iran yana mai jaddada cewa wajibi ne kasashen musulmi su karfafa hadin kai da hadin kai don mayar da martani ga ayyukan gwamnatin sahyoniyawan, inda ya ce: Wajibi ne kasashen musulmi su tsaya tsayin daka tare da daukar matakai na zahiri a fagen tattalin arziki, al’adu da zamantakewa, yanke alakarsu da gwamnatin sahyoniyawan.

Masoud Pezeshkian shugaban kasar Iran a jiya litinin kafin ya tashi zuwa kasar Qatar domin halartar taron gaggawa na kungiyar hadin kan kasashen musulmi ta OIC da kungiyar hadin kan kasashen larabawa dangane da harin da gwamnatin sahyoniyawan ta kai wa birnin Doha, ya bayyana cewa: “Gwamnatin yahudawan sahyoniya ba ta amince da wani iyaka ga kanta ba, kuma tare da goyon bayan Amurka, ta kai hare-hare kan kasashen musulmi da dama da suka hada da Qatar, Lebanon, Iraq, Iran, Yemen da kuma kasashen turai suna goyon bayan wadannan kasashen duniya. ayyuka.”

Shugaban na Iran ya kara da cewa: Gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila tana aiwatar da kisan kiyashi a zirin Gaza, tare da la’antar mata da yara da tsoffi, abin takaicin shi ne kasashen yammacin turai, ta hanyar goyon bayansu da kuma tanade-tanaden da suke baiwa gwamnatin wariyar launin fata ta sahyoniyawa, sun halasta wadannan ayyukan.

Pezeshkian, yayin da yake bayyana fatan sakamakon taron gaggawa na OIC da shugabannin kungiyar kasashen Larabawa, ya jaddada cewa: Dole ne kasashen musulmi su karfafa hadin kai da hadin kai don mayar da martani ga ayyukan gwamnatin sahyoniyawan da kuma kokarin tabbatar da cewa ana aiwatar da laifuffukan wannan gwamnati a dandalin kasa da kasa da na shari’a, ya kamata kasashen musulmi su tsaya tsayin daka, ta hanyar daukar matakai masu amfani a fannin tattalin arziki, al’adu, da zamantakewar al’ummar Sahayoniya.

Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa, ya nakalto daga shafin sadarwa na yanar gizo na jaridar Pars Today cewa, a yammacin ranar Talata 9 ga watan Satumba, jiragen kasar Isra’ila sun keta sararin samaniyar kasar Qatar, inda suka yi ruwan bama-bamai a yankin Katara na birnin Doha, babban birnin kasar, inda wata babbar tawaga ta Hamas karkashin jagorancin Khalil al-Hayya ke ganawa.

A mayar da martani, an gudanar da taron ministocin harkokin wajen kungiyar OIC a jiya Lahadi a birnin Doha, wanda ya samu halartar ministan harkokin wajen kasar Iran, domin tinkarar matsalar wuce gona da iri da sojojin gwamnatin sahyoniyawan suke kaiwa kasar Qatar. Wannan taron dai ya kasance share fage ga taron kasashen musulmi da na larabawa, wanda aka shirya gudanarwa a yau litinin tare da halartar Masoud Pezeshkian shugaban jamhuriyar musulinci ta Iran.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai September 15, 2025 Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar September 15, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha September 15, 2025  Dan Kasar Iran Mai Kirkira Ya Sami Kyautar Yabo A Kasar China September 15, 2025 Fizishkiyan:  Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI September 15, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha September 15, 2025 Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA September 15, 2025 Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar September 15, 2025 Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000 September 15, 2025 Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Baje Kolin Sin Da ASEAN Ya Fadada Matsayar Bai Daya Ta Cudanyar Sassa Daban Daban
  • Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
  • Iran Ta Bayyana Abubuwan Da Bata Amince Da Su Ba A Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar OIC A Birnin Doha
  • Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
  • Kungiyar Human Rights Watch; Isra’ila Ta Kashe ‘Yan Jarida Fiye Da 30 A Kasar Yemen Ne Da Gangan  
  • An Fara Taron Hukumar Makamashin Nukliya Ta Duniya IAEA Karo Na 69 A Birnin Vienna
  • Taron Doha: Daga matakin Allawadai zuwa matakan kalubalantar laifukan Isra’ila
  • Pezeshkian: Ya kamata kasashen musulmi su yanke alaka da gwamnatin sahyoniya tare da kiyaye hadin kai
  • Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
  • Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces