Bugu da kari, akwai kuma masu kiwon Tarwada a gonar da sama da su 600, wadanda aka rage yawan adadinsu daga 1,327 zuwa 600, bayan bullar cutar annobar Korona, saboda kalubalen ci gaba da gudanar da sauran ayyukan gonar.

A shekarar 2024, masu kiwon Tarwadar a gonar; sun samar da Tarwadar da yawanta ya kai kimanin tan 1,700, wadda kuma aka kiyasata cewa; kudinta ya kai na Naira biliyan 4.

5.

Wannan ba karamin ci gaba ba ne, musamman duba da cewa; gonar ta kasance abin koyi ga sauran kungiyoyin da ke kiwon Tarwada a daukacin fadin wannan kasa.

Bisa wannan nasarori da gonar ta samar, hakan ya nuna yadda take ci gaba da samun yabo daga kasashen duniya, cikin masu yabon har da Hukumar Bunkasa Samar da Abinci da Habaka Aikin Gona (FAO) da kuma wani yabon daga wurin sauran hukumomin kasa da kasa da ke tallafa wa fannin.

Ya zuwa yanzu, Hukumar ta FAO; ta wanzar da wani aiki na kiwon Kifi da ake kira da ‘FISH4ACP’, wanda kuma Tarayyar Turai (EU) da Gidauniyar Giz ke zuba kudade a cikin aikin, musamman domin tabatar da ganin an samar da damar samun kudade da taimakawa wajen gudanar da yin bincike a fannin.

Babban Jami’in gudanar da aikin ‘FISH4ACP’ da ke Hukumar ta FAO, Dakta Abubakar Usman ya bayyana cewa; an samu kyakkyawan sakamako a binciken da aka gudanar, wanda kuma har yanzu ake ci gaba da amfana da shi sakamakon binciken, musamman ganin cewa; bincken zai taimaka wajen rage kalubalen da ake fuskanta na tsadar abincin ciyar da Tarwadar zuwa sama da kashi 20 cikin 100.

Shi kuwa, babban shugaba a shirin nan na IDIPR, Marcus Adeniyi, a tattaunawar da aka yi da shi a gonar da ke kauyen Eriwe a Ijebu Ode, ya sanar da cewa, kungiyar ta masu kiwon Tarwadar; na kara tumbatsa ne matuka.

Ya sanar da cewa, duk yawan Tarwadar da aka sayar, ana tura kudaden cinikin ne kai tsaye zuwa ga asusun ajiyar kudade.

A cewar Adeniyi, Tarwadar da ake da ita a yanzu a gonar; ta kai ta kimanin Naira biliyan shida, inda ya kara da cewa; bisa bayanansu a zango farko na shekarar 2025, an sayar da Tarwada sama da tan 600.

“Idan har a shekarar 2024, mun samar da tan 1,700 na Tarwada, wadda kudinta ya kai kimanin Naira biliyan 4.5, a wannan shekarar ta 2025, muna sa ran adadin zai zarta wannnan; wanda zai iya kai wa kimanin Naira biliyan shida,” in ji Adeniyi.

Kazalika, ya bayyana cewa; muna sa ran samar da yawan Tarwadar da za ta kai sama da tan 2000, kafin karshen shekarar 2025.

Bugu da kari, ya bayyana cewa; kungiyar a kowane zango daya na shekara, tana shirya wa masu kiwon Tarwadar horo na musamman, inda sabbin shiga cikin kungiyar ke biyan Naira 2,500, domin yin rijista da su.

Ya ce, kungiyar na raba wa ‘ya’yanta wuraren kiwon Tarwadar, inda ake cazar su Naira 15,000.

Kazalika, bayan mai kiwon ya samar da Tarwada ta farko, kungiyar za ta ba shi, rancen Naira miliyan biyu, inda rancen zai kasance kashi 18 cikin 100 na kudin ruwa, har zuwa karshen shekara daya.

Shi kuwa, wani mai kiwon Tarwadar mai suna Oyinade Matthew Adeneye, wanda kuma yake tafiyar da Kwamin kiwon Tarwadar guda sha biyu, wanda kuma tun a shekarar 2008 yake yin kiwon a yankin ya sanar da cewa; yanzu haka; yana da sama da Tarwada 30,000 wadanda kuma suke kan matakai daban-daban.

A cewarsa, aikin na ‘FISH4ACP’, zai taimaka wajen karfafa samar da ilimin yadda za a rika kula da kiwon Tarwada da kuma magance kalubalen da masu kiwon ke fuskanta na rashin samun riba mai yawa.

Adeneye ya ci gaba da cewa, aikin zai kuma samar da sauyi a fagen kiwon na Tarwada tare kuma da samar da damar samun rancen kudaden yin kiwon.

Manufar aikin na ‘FISH4ACP’ dai, zai kasance wajen bayar da gudunmawar ci gaba da kiwon Tarwadar da kuma samun kudaden shiga.

A yanzu haka, ana gudanar da wannan aiki a kasashe sha biyu, inda ake gudanar da aikin a kasashe tara da ke Nahiyar Afirka biyu, a kuma yankin Caribbean, daya kuma a tekun Pacific, wanda aka zuba kimanin Yuro miliyan 40 tare da kuma karin wasu kudade daga Gwamnatin Kasar Jamus.

A bangaren Nijeriya kuwa, an mayar da hankali ne a fannin na kiwon Tarwada, domin samun riba; wanda kuma aka wanzar da aikin a shiyoyin siyasa shida na fadin kasar nan.

Jihohin da aka wanzar da ayyukan su ne, Jihohin Kudu Maso Yamma, inda ake wanzar da aikin a Jihar Ogun, sai kuma a Kudu Maso Kudu da ake wanzar da aikin a Jihar Delta.

Sauran su ne; Kudu Maso Gabas da kuma Arewa Ta Tsakiya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kimanin Naira biliyan masu kiwon Tarwada kiwon Tarwadar Tarwadar da

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers

Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sanar da janye dokar ta-baci a Jihar Rivers daga ƙarfe 12 na daren 17 ga watan Satumban 2025.

Shugaban Ƙasar, a wata sanarwa da ya sanya wa hannu, ya ce dokar ta-bacin da ta dakatar da Gwamna, Mataimakiyarsa, da ‘yan majalisar dokokin jihar na tsawon watanni shida ta cimma manufarta na dawo da zaman lafiya a jihar.

Tinubu ya bayyana cewa ya yi amfani da Sashe na 305 na Kundin Tsarin Mulkin 1999 ne a watan Maris na 2025 sakamakon durƙushewar mulki a Jihar Rivers.

A cewarsa, rashin jituwa tsakanin Gwamna Siminalayi Fubara da Majalisar Dokokin Jihar, da kuma lalata muhimman kadarorin gwamnati sun jefa jihar cikin rikici.

“Lamarin ya kai ga Babbar Kotun Ƙoli ta bayyana a ɗaya daga cikin hukuncinta cewa babu gwamnati a Jihar Rivers.” In ji Shugaban Ƙasa.

Ya gode wa Majalisar Ƙasa bisa amincewa da wannan sanarwa, tare da yabawa Sarakuna da jama’ar jihar bisa haɗin kan da suka bayar.

Tinubu ya kuma yaba wa  masu adawa da suka kalubalanci wannan mataki a kotu, yana cewa wannan shi ma wani ɓangare ne na dimokuraɗiyya.

Da yake magana kan sabuwar fahimta tsakanin manyan ‘yan siyasa a jihar, Shugaban Ƙasa ya ce babu dalilin ƙara tsawaita dokar ta-bacin.

Ya bayyana cewa Gwamna Siminalayi Fubara, da Mataimakiyarsa Ngozi Nma Odu, da Shugaban Majalisar Dokoki Martins Amaewhule da dukkan mambobin majalisar jihar za su koma bakin aiki daga 18 ga Satumban 2025.

Tinubu ya yi kira ga shugabannin siyasa a faɗin Najeriya da su ƙarfafa zaman lafiya da haɗin kai domin isar da fa’idodin dimokuraɗiyya ga al’umma.

 

Daga Bello Wakili

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa
  • Kakakin Majalisar Jigawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya, Tawagar Jami’an Tsaronsa Sun Ji Rauni A Wani Hatsari A Jihar 
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • Ɗangote zai gina ɗakunan kwanan ɗalibai 250  a Jami’ar Ilorin