Aminiya:
2025-07-31@16:46:58 GMT

Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe

Published: 15th, June 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan jihar Gombe, ta tabbatar da mutuwar mutum biyar da kuma jikkatar wasu 13, sakamakon tashin wutar lantarki a unguwar Tudun-Wada, Pantami a jihar.

Wutar ta tashi ne da safiyar ranar Asabar sakamakon matsala da ta taso daga wata tiransifoma a yankin, kamar yadda kakakin ’yan sandan jihar, DSP Buhari Abdullahi, ya bayyana.

Sojoji sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa

Cikin waɗanda suka rasa rayukansu har da Babban Sakatare na Ma’aikatar Ayyuka ta Musamman ta jihar, Alhaji Muhammad Yusuf Kulani, tare da ’ya’yansa da wasu mazauna unguwar.

Marigayin shi ne shugaban ƙungiyar ƙwararrun akantoci ta Jihar Gombe (ANAN).

’Yan sanda daga ofishin Low-Cost sun isa wajen don tabbatar da tsaro da kuma kai waɗanda suka jikkata zuwa asibiti.

Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, Bello Yahaya, ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan mamatan.

Ya kuma ce za su gudanar da cikakken bincike domin gano musabbabin tashin wutar da kuma ɗaukar matakan kare faruwar hakan a gaba.

Ya kuma roƙi al’umma da su kasance masu bin doka tare da bayar da haɗin kai yayin gudanar da binciken.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Rauni Wutar Lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina

An ceto dukkanin mutane 14 ba tare da wani ya ji rauni ba, amma abin baƙin ciki, wani matashi ɗan shekara 27 mai suna Abba daga garin Funtua ya rasa ransa kafin isowar ’yansanda.

A wani lamari da ya faru a ranar 28 ga watan Yuli da misalin ƙarfe 11:27 na dare, an sake kiran ’yansanda daga ƙauyen Zagaizagi, inda aka sanar da su cewa wasu ’yan bindiga sum hari tare da sace wasu mutane ƙauyen.

’Yansanda sun isa wajen suka gwabza da ’yan bindigar, kuma sun samu nasarar ceto wasu mutane 14 da kuma ƙwato shanun da aka sace guda biyu.

Amma, mutane biyu daga cikin mazauna ƙauyen sun rasa rayukansu a harin.

Rundunar ta ce har yanzu tana ci gaba da ƙoƙarin kamo ’yan bindigar da suka tsere.

Kwamishinan ’yansandan, CP Bello Shehu, ya yaba wa jami’ansa bisa jarumtaka da suka nuna.

Ya kuma buƙaci jama’a da su ci gaba da bai wa ’yansanda sahihan bayanai a kan lokaci.

Ya tabbatar da cewa rundunar za ta ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a faɗin jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Samar da makamashi mai tsafta na zamani shi ne fatanmu — Guterres
  • ‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu 
  • Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 
  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina
  • Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya
  • Remi Tinubu ta ba da tallafin Naira biliyan ɗaya ga waɗanda harin Benuwe ya shafa
  • Jami’ar Jihar Gombe za ta fara sabbin darussa 6 a fannin noma
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a Alkaleri
  • ‘Yan Sanda A Kano Sun Kama Kasurgumin Dan Fashin Nan Barga Da Wasu Mutum 14
  • Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa