Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Shaida Gamsuwa Da Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
Published: 14th, June 2025 GMT
Yayin da taro na biyu na tattauna hadin gwiwar Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya ke kara matsowa, sakamakon kuri’un jin ra’ayin jama’a da kafar CGTN ta kasar Sin ta gudanar, sun nuna gamsuwa da hadin gwiwa bisa matsayin koli dake tsakanin Sin da kasashen nan biyar na yankin tsakiyar Asiya, a matsayin wata hadaka ta al’umma mai kyakkyawar makomar bil’Adama, wadda ke kara shigar da sabon kuzari, na daidaito cikin yanayin duniya dake kara shiga yanayin tangal-tangal.
Tun dai taro na farko na tattauna hadin gwiwar Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya, hadin gwiwa tsakanin Sin da kasashen biyar ya shiga wani sabon zango na ci gaba. Har ma kuri’un na jin ra’ayin jama’a suka nuna yadda kaso 90.4 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyinsu, ke ganin tsarin taron shugabannin Sin da kasashen na tsakiyar Asiya ya taka rawar gani a wannan fanni.
Kazalika, kaso 92 bisa dari na ganin ta hanyar mayar da kasashen tsakiyar Asiya daya daga muhimman jigon diflomasiyyar makwaftanta, Sin ta samar da wasu damammaki ga kasashen tsakiyar Asiya, na cimma burin sauye-sauye, da ci gaba da yin babban tasiri a shiyyarsu. Yayin da yanayin yankunan Turai da Asiya ke kara sauyawa cikin hanzari, kaso 88.1 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyinsu na ganin gina al’ummun Sin da tsakiyar Asiya masu makomar bai daya, na da muhimmancin gaske wajen karfafa tsare-tsaren kasashen tsakiyar Asiya, na samar da ‘yanci da daidaiton shiyyarsu. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: kasashen tsakiyar Asiya
এছাড়াও পড়ুন:
Za a rataye wanda ya kashe ɗan uwansa a Ekiti
Wata babbar kotun Jihar Ekiti da ke zamanta a Ado Ekiti ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataye wani mai suna Stephen Adamu mai shekara 34 bisa laifin kashe ɗan uwansa.
An gurfanar da wanda ake tuhuma a gaban mai shari’a Adekunle Adeleye a ranar 31 ga watan Junairu, 2025, kan tuhumar kashe wani David Adamu, a sashi na 234 na dokar laifuka ta jihar Ekiti 2021.
Gobara ta tashi a babban kanti a Abuja Ƙasashe 12 da suka samu tikitin Kofin Nahiyyar Afrika na mataDomin tabbatar da ƙarar sa, mai gabatar da ƙara Funmi Bello, ya kira shaidu shida da waɗanda ake ƙara da su gabatar da jawabi, da fom ɗin shaida da kuma wuƙa a matsayin nunin shaida.
Wanda ake tuhumar ya yi magana ta bakin Lauyansa, S.K Idowu, kuma bai kira wani shaida ba.
Da yake yanke hukuncin, mai shari’a Adeleye ya ce daga dukkan yanayin wannan shari’a, Stephen Adamu ya daɓa wa David Adamu wuƙa a wuya.
“Na sami wanda ake tuhuma da laifi kamar yadda ake tuhumarsa, wanda ake ƙara Stephen Adamu an yanke masa hukuncin kisa ta hanyar rataya,” in ji shi.