HausaTv:
2025-11-22@04:45:00 GMT

Araghchi: Gwamnatin Amurka ta haramta wa Irakawa samun wutar lantarki

Published: 11th, March 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya yi Allah-wadai da matakin da gwamnatin Amurka ta dauka na haramtawa  al’ummar Iraki ‘yancinsu na samun wutar lantarki, da ma wasu ababen more rayuwa.

“Muna tare da al’ummar Iraki, kuma mun tabbatar da alkawarinmu ga gwamnatin Iraki na ba da hadin kai wajen tinkarar matakan da Amurka ta dauka ba bisa ka’ida ba,” in ji Araghchi a wani sakon da ya wallafa a shafin X.

Kamfanin dillancin labaran reuters ya nakalto wani babban jami’an makamashi  a kasar Iraki yana cewa, a halin yanzu Iraki ba ta da wasu hanyoyin da za su maye gurbin makamashin da ake shigowa dashi  daga kasar Iran, lamarin da zai haifar da babban kalubale wajen biyan bukatar wutar lantarki a cikin gida musamman a lokacin bazara.

Tun da farko a ranar Lahadin da ta gabata, wani jami’in Amurka ya tabbatar da cewa Washington ta yanke shawarar kin sabunta yarjejeniyar da ta bai wa Iraki damar sayen wutar lantarki daga Iran.

Wani babban jami’in ma’aikatar wutar lantarki ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa “Gwamnati ta fara aiwatar da matakan gaggawa don rage tasirin matakin da Amurka ta dauka kan samar da wutar lantarki a Iraki.”

Wa’adin ya kare a ranar Asabar din da ta gabata, yayin da kumama’aikatar harkokin wajen Amurka ba ta tsawaita wa’adin ba, kamar yadda wata sanarwa daga ofishin jakadancin Amurka da ke Bagadaza ta bayyana.

Wannan shawarar wani bangare ne na matakin matsin lamba na Shugaba Donald Trump kan Iran, da nufin dakatar da abin da yake kira barazanar nukiliyar Iran, da dakile shirinta na makami mai linzami da kuma hana ta tallafawa kungiyoyin ‘yan gwagwarmaya a yankin.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: wutar lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Hisbah Ta Rufe Wani Wuri da Ake Zargin Ana Aikata Badala A Kano

Daga  Khadijah Aliyu 

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kama wasu samari bakwai da ke shiga irin ta mata da aikata badala a wani shahararren gurin nishadi da ke kan titin Zoo Road a karamar hukumar Kano Municipal.

Yayin tabbatar da faruwar lamarin ga Rediyon Nijeriya, Mataimakin Kwamanda Janar na hukumar Hisbah, Sheikh Mujahid Aminudeen Abubakar, ya ce an kama samarin da ke kasa da shekaru 23 bayan samun bayanan sirri daga wani mai kishin ƙasa.

Mai bayar da bayanan ya sanar da cewa mmatasn da aka fi sani da ‘Yan Daudu, suna yawan zuwa wurin, inda ake zargin cewa motocin mutane daban-daban ke zuwa su ɗauke su.

Sheikh Mujahid ya bayyana cewa binciken farko ya nuna cewa matasan sun fito ne daga jihohin Kogi, Bauchi da Kano.

Ya ƙara da cewa yayin gudanar da aikin, jami’an Hisbah sun kuma kama wani saurayi da wata budurwa da aka same su tare a cikin babur mai ƙafafu uku, sannan kuma an gano wata yarinya da aka ce ta bace a Sakkwato, aka kuma maida ta ga iyayenta.

Mataimakin Kwamanda Janar din ya ƙara da cewa hukumar za ta rufe wurin nishadin saboda zargin  ɓoye ƙananan yara da ke aikata munanan ayyuka.

Ya ce za a mika matasan da aka kama tare da masu kula da wurin ga hukumomin da suka dace domin ci gaba da daukar mataki.

Sheikh Mujahid ya tabbatar da jajircewar Hisbah na kawar da dukkan nau’o’in munanan dabi’u a jihar, tare da kira ga jama’a da su rika kai rahoton duk wata matsala ko abin da suke shakku ga hukumar Hisbah ko wasu hukumomi da suka dace.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Jaddada Goyon Bayan Gwamnatin Tarayya Ga Muhimman Tsare-Tsaren Kaduna.
  • Hukumar Hisbah Ta Rufe Wani Wuri da Ake Zargin Ana Aikata Badala A Kano
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Dalibai Mata 25 a Jihar Kebbi 
  • Babu wani addini da matsalar tsaron Nijeriya ta ƙyale — Fafaroma
  • Sai da Kwankwaso APC za ta iya samun nasara a 2027 — NNPP
  • Wayar wutar lantarki ta kashe mutum 4 a wajen cashiya a Legas
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Iran Ta Ce: A Yanzu Babu Wata Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Gobara ta laƙume kasuwar Katako a Gombe
  • Iraki : Jam’iyyar firaminista, Shia al-Soudani ta samu rinjaye a Majalisar dokoki
  • DAGA LARABA: Hanyoyin Da Suka Kamata A Bi Wajen Ceto Daliban Kebbi Da Aka Sace