HausaTv:
2025-03-16@00:04:10 GMT

Araghchi: Gwamnatin Amurka ta haramta wa Irakawa samun wutar lantarki

Published: 11th, March 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya yi Allah-wadai da matakin da gwamnatin Amurka ta dauka na haramtawa  al’ummar Iraki ‘yancinsu na samun wutar lantarki, da ma wasu ababen more rayuwa.

“Muna tare da al’ummar Iraki, kuma mun tabbatar da alkawarinmu ga gwamnatin Iraki na ba da hadin kai wajen tinkarar matakan da Amurka ta dauka ba bisa ka’ida ba,” in ji Araghchi a wani sakon da ya wallafa a shafin X.

Kamfanin dillancin labaran reuters ya nakalto wani babban jami’an makamashi  a kasar Iraki yana cewa, a halin yanzu Iraki ba ta da wasu hanyoyin da za su maye gurbin makamashin da ake shigowa dashi  daga kasar Iran, lamarin da zai haifar da babban kalubale wajen biyan bukatar wutar lantarki a cikin gida musamman a lokacin bazara.

Tun da farko a ranar Lahadin da ta gabata, wani jami’in Amurka ya tabbatar da cewa Washington ta yanke shawarar kin sabunta yarjejeniyar da ta bai wa Iraki damar sayen wutar lantarki daga Iran.

Wani babban jami’in ma’aikatar wutar lantarki ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Reuters cewa “Gwamnati ta fara aiwatar da matakan gaggawa don rage tasirin matakin da Amurka ta dauka kan samar da wutar lantarki a Iraki.”

Wa’adin ya kare a ranar Asabar din da ta gabata, yayin da kumama’aikatar harkokin wajen Amurka ba ta tsawaita wa’adin ba, kamar yadda wata sanarwa daga ofishin jakadancin Amurka da ke Bagadaza ta bayyana.

Wannan shawarar wani bangare ne na matakin matsin lamba na Shugaba Donald Trump kan Iran, da nufin dakatar da abin da yake kira barazanar nukiliyar Iran, da dakile shirinta na makami mai linzami da kuma hana ta tallafawa kungiyoyin ‘yan gwagwarmaya a yankin.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: wutar lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

Jagora : kiran Trump, na tattaunawa Da Iran yaudarar duniya ne

Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran, Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya ce kiran da shugaban Amurka Donald Trump ya yi na tattauanwa da Iran ba komai ba ne illa wani yunkuri na yaudarar al’ummar duniya.

 “Mun zauna tsawon shekaru muna tattaunawa, mun zamna da su teburin tattaunawa, bayan hakan shi wannan mutumin ya yayyaga yarjejeniyar da aka sanya wa hannu,” kamar yadda jagoran ya bayyana yayin da yake jawabi ga taron dalibai a birnin Tehran a jiya Laraba.

“tunda mu ka ga baya girmama yarjejeniya, menene ma’anar yin shawarwari kuma ?”

“Saboda haka, kiraye-kirayen yin shawarwarin da tattaunawa na da nufin yaudarar  jama’a na duniya.” Inji jagoran.

Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya ce “Idan manufar tattaunawar ita ce a dage takunkumin, yin shawarwari da wannan gwamnatin Amurka, ba za ta cire takunkumin ba. Hakan zai sa takunkumin ya kara tsananta tare da kara matsin lamba,” in ji Jagoran.

Yayin da yake mayar da martani kan zargin da kasashen yammacin duniya ke yi na cewa Tehran na neman makaman nukiliya, Jagoran ya sake jaddada cewa Iran ba ta son kera makaman kare dangi, inda ya kara da cewa da ta yi niyyar yin hakan da ta yi shi ya zuwa yanzu.

“An ce ‘ba za mu bar Iran ta samu makaman nukiliya ba.’ Da muna son kera makaman nukiliya, da Amurka ba za ta hana mu ba.

Gaskiyar ita ce ba mu da makaman nukiliya, saboda mu da kanmu ba ma son su saboda wasu dalilai.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi : Iran a shirye take ta shiga tattaunawa da Turawa bisa mutunta juna
  • Gwamnatin Trump na tunanin hana ‘yan kasashe kusan 40 ciki har da Iran shiga Amurka
  •  Iraki: An Kashe Shugaban Kungiyar “Da’esh” Na Iraki Abdullahi Makki
  • Nageriya ta Maida Martani Kan Zargin Kissin Kiristoce A Kasar,Wanada Gwamnatin Amurka Ta Yi Mata
  • Sin Ba Za Ta Taba Amincewa Da Ayyukan ’Yan Aware Ba 
  • Iran ta yi kakkausar suka kan sabon takunkumin Amurka
  • Sudan Ta Haramta Shigar Da Kayayyakin Daga Kenya
  • HKI Tana Cigaba Da Keta Tsagaita Wutar Yaki A Lebanon
  • Yadda ’yan Boko Haram suka sha da ƙyar a hannun tawagar Gwamna Zulum
  • Jagora : kiran Trump, na tattaunawa Da Iran yaudarar duniya ne