HausaTv:
2025-06-14@09:52:49 GMT

Jagora: “Yan Sahayoniya Su Saurari Ukuba Mai Tsanani

Published: 13th, June 2025 GMT

Jagoran juyin juya halin musulinci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamnei ya fitar da bayani a yau juma’a da a ciki ya yi wa ‘yan sahayoniya alkawalin fuskantar ukuba mai tsanani.

Bayanin na jagora ya kunshi cewa:

Da sunan Allah Mai Rahama Mai Jin Kai

Ya Ku Al’ummar Iran Masu Girma

Da safiyar yau, ‘yan sahayoniya sun miko hannuwansu da suke jike da jini, domin tafka laifuka a cikin kasarmu.

 Sun kuma sake bayyana hakikanin dabi’arsu mummuna fiye da kowane lokaci a baya,  su ka kai wa  gidajen fararen hula hari. A dalilin haka, wannan haramtacciyar kasar ta saurari sakamako mai tsanani.

Su kuma  sani cewa; Sojojin Jamhuriyar musulunci masu karfi ba za su kyale su ba da yardar Allah. A yayin wannan harin kwamandoji da dama da masana sun yi shahada.

Wannan laifin da ‘yan sahayoniya su ka tafka, ya sa sun shirya wa kansu makoma mai tsanani da daci, za su kuma ga hakan babu tantanma.

Sayyid Ali Khamnei

13/06/2025

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 Iran Za Ta Kara Yawan Sanadarin Urani’um Da Take Tacewa A Wuri Na Sirri

A wani bayani na hadin gwiwa da hukumar makamashin Nukiliya ta Iran da kuma ma’aikatar harkokin wajen Iran su ka fitar, sun bayar da umarnin a bude wani wuri na daban na sirri domin ci gaba da tace sanadarin Urani’um, sannan kuma a maye gurbin bututu tace sanadarin mai  mataki na daya, da mai mataki na shida a cibiyar “Pardo.”

Bayanin dai ya zo ne a matsayin mayar da martani ga sanarwar da ta fito daga kwamitin alkalai na hukumar makamashin Nukiliya ta kasa da kasa akan Iran.

Bugu da kari, bayanin na Iran ya kuma ce; A kodayaushe jamhuriyar musulunci ta Iran tana aiki da nauyin da ya rataya a wuyanta, kuma har ya zuwa yanzu babu wani rahoto na hukumar wanda ya bayyana cewa; Iran ba ta aiki da ka’idojin hana yaduwar makaman Nukiliya.”

Haka nan kuma bayanin ya ambaci cewa; Tare da cewa Iran tana daukar rahoton da cewa na siyasa ne, wanda Amurka da kasashen turai suke amfani da hukumar a matsayin makami, ba tare da dogaro da wani dalili na ilimi ba.

Har ila yau Iran din ta zargi Amurka da kasashen na turai da wuce gona da iri wajen tsara rahoton da yake cin karo da rahoton da shugaban hukumar ta makamashin Nukiliya ya fitar, wanda bai sami wani abu mai  shiga duhu ba a cikin Shirin na Iran na zama lafiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bude Kofofin Jahannama Ga Yahudawan Sahayoniyya
  • Jagora: Sojojin Iran ba zasu sararawa Isra’ila ba
  • Birgediya Pakphur: Nan Gaba Kadan Za A Budewa “Isra’ila” Kofofin Jahannama
  • Sakon Jagora : Isra’ila ta jira hukunci mai tsanani bayan hari kan Iran
  • IRGC : Iran a shirye take na tunkarar duk wani yanayi
  •  Iran Za Ta Kara Yawan Sanadarin Urani’um Da Take Tacewa A Wuri Na Sirri
  • Salami: Babu Inda Ba Za Mu Iya Kai Wa Hari Ba A Fadin HKI
  • Kasashen Iran Masar Da Kuma Omman Sun Gudanar Da Taro A Oslo
  • Jagora Ya Bambance Tsakanin Majalisun Dokokin Kasashe A Fagen Gudanar Da Ayyukan Kasa