An rufe taron ministocin Sin da Afirka mai tabbatar da ci gaban hadin gwiwar da aka samu a dandalin tattaunawar hadin kan Sin da Afirka wato FOCAC, wanda aka gudanar daga ranekun 10 zuwa 12 a birnin Changsha na lardin Hunan, matakin da ya bayar da sabbin damammaki ga kasashen Afirka, bisa shirin “manyan ayyuka 10 na abota tsakanin Sin da Afirka”.

Sa’an nan, bayan an kammala taron, nan take, an kaddamar da bikin baje kolin kayayyaki hajojin Sin da Afirka karo na 4, duk a birnin Changsha, matakin da ya zamo daya daga cikin jerin ayyukan da ake gudanar da su don aiwatar da shirin “manyan ayyuka 10”, inda aka baje kolin ci gaban da aka samu, da tattara damammaki da albarkatu wuri guda, domin gaggauta samun ingantacciyar bunkasar hadin gwiwar Sin da Afrika a bangaren ciniki da tattalin arziki.

A cikin shekaru 25 da suka gabata, tun kafuwar FOCAC a shekarar 2000, yawan kudin kayayyakin da ake shigarwa da na fitarwa tsakanin Sin da Afirka ya karu zuwa dalar Amurka biliyan 292.4 a shekarar 2024 daga dalar biliyan 13.9 a 2000, inda adadin ya karu da fiye da ninki 20. Kana a cikin wasikar da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya aika don taya murnar cimma nasarar gudanar da taron ministoci na wannan karo, Xi ya sanar da shirin yafe harajin kwastam na kaso 100% a kan kayayyakin kasashen Afirka 53, wadanda suka kulla dangantakar diflomasiyya da Sin, matakin da zai kara saukaka wa kasashen Afirka a fannin fitar da kayayyakinsu zuwa kasar Sin.

Kazalika, a farkon watanni 5 na bana, yawan kudin da Sin ta kashe wajen shigo da kayayyakin Afrika zuwa cikin kasarta ya kai dalar Amurka biliyan 50.6, adadin da ya karu da kashi 1.6% bisa na makamancin lokacin bara. Hakan ya ba kasashen Afirka damar more babbar kasuwar Sin.

Hadin gwiwar Sin da Afirka na kara habaka, duba da yadda ake aiwatar da hakikanan matakai don tabbatar da manyan tsare-tsare da aka cimma, tare da mai da hankali matuka kan amfanar da al’ummun Afirka, da inganta karfin kasashen Afirka na samun bunkasuwa bisa dogaro da kai. Ma iya cewa, hadin gwiwar bangarorin Afirka da Sin ta fuskar ciniki da tattalin arizki na cikin wani yanayi mai armashi da dorewa, duk da kalubaloli, da sauye-sauyen yanayin da ake fuskanta a duniya, abin da sa ake samun cikakken kwarin gwiwa bisa hadin gwiwar kasashe masu tasowa da bunkasar duniya baki daya. (Mai zane da rubutu:MINA)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: hadin gwiwar

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)

Ba tare da saninmu ba, yawancin al’ummar Afirka musamman ma naYammacin Afirka suna fama da abinda ake kira da suna irin hali ko yanayin da aka shiga sanadiyar lamarin cinikin Bayi.Bayan shekara 100 da aka yi daga shekarar 1801 zuwa 1901, an yi wani kokarin da ake yi ma kallon tamkar wani takune na yadda za’a kubuta daga irin cin fuskar da ake yi kowace rana.

Kafin dai a tsunduma sosai cikin lamarin cinikin Bayi, yana da matukar kyau a fara yin bayani kan yadda abin ya fara:Lamarin cinikin Bayi ba manufa bace ta Yammacin Turai.Duk lamarin ya zarce wani hasashen da za’a iya yi ko wani rubutun,da aka yi aka aje.Idan kuma aka duba ta bangaren nahiyar Afirka ita kanta, sha’anin cinikin Bayi ya kasance nae kafin zuwa Turawa shekaru darurra da suka gabata,lamarin kuma yana ci gaba har zuwa halin da ake ciki yanzu ,ana iya tunawa da yadda Bayin da aka saya a nahiyar Afirka ake tafiya da su ta hanyar Sahara wadda take da Yashi,ta haka ne aka fara musanyar mutane,a bada su ,sannan a amshi wasu abubuwa”.

Afirka, a matsayinta na nahiya ita ma ta dandana kudarta idan ana maganatr cinikin Bayi har zuwa shenture 14 wanda ya zarce shekara 1000 ke nan:10 ga duniyar Larabawa,sai kuma 4 ga sauran yammacin Turai. Ciniki Bayi na bangaren Larabawa ya far ne a karni na 8 hakan ta kasance ne saboda yadda addinin musulunci ya hana Musulmai daga bautar da ‘yan’uwansu. Duk da an hana hakan bukatar mutane su rika yin wasu ayyuka,don haka shi yasa Larabawa suke zuwa nahiyar Afirka domin su samu Bayin.Da farko sun tsaya ta gabas ta gabar ruwa na, Rift Balley, amma yayin da suke kasuwanci, sai suka rika yada addininsu na musulunci. Wannan ya nuan ke nan wurin da yake ana ta lamarin fataucin Bayi,ya zama yanzu babu yadda za su yi su samu Bayi daga can,don haka sannu a hankali sai suka maida akalarsu zuwa yammacin Afirka.domin idon su ya fara budewa saboda ai addinin musulunci ya hana cinikin Bayi. Wannan shi yake nuna duk yadda Larabawa suke bukatar samun ‘yan Afirka a matsayin Bayi ya zo karshe.

Abu daya wanda yake kamar sun yi kama da juna tsakaanin Larabawa da Yammacin Turai shi ne suna yin amfani ne da addini, Musulunci da Kiristanci domin su samu bakin bada dalilin da yasa suke kasuwancin mutane.A kokarin da muke na nuna yin kama da juna, sai mun yi bayani dangane da bambancin, tsakanin kasuwancin na hanyar da ake bi ta Yashi, da kuma ta wani babban Kogi da kuma na ake bi ta babban ruwa ne.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Shaida Gamsuwa Da Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Tsakiyar Asiya
  • HKI Ta Rufe Filin Saukar Jiragen Sama Na Ben Gorion Tare Da Dauke Jiragenta  Zuwa Waje
  • An Samu Babban Canji Kan Tsarin Ciniki A Tsakanin Sin Da Afirka
  • Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (1)
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci
  • Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
  • Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje
  • Nijeriya Ce Ta 3 A Manyan Kasashe Masu Karfin Masana’antu 10 Na Afirka
  • ICPC Ta Gurfanar Da Ma’aikacin Kotu Bisa Badakalar Naira Miliyan 9.2