Leadership News Hausa:
2025-07-29@05:08:12 GMT

Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai

Published: 13th, June 2025 GMT

Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai

A cewar Bawa, gwamnatocin da a karkashinsu aka wawashe dukiyar kasa, su ne na Mulkin Tsohon Shugaban Kasa Olusegun Obasanjo (daga 1999 zuwa 2006), sai Marigayi Shugaba Umaru Musa Yar’Adua (daga 2007 zuwa 2009), kazalika a mulkin Shugaba Goodluck Jonathan daga (2010 zuwa 2014), sai kuma mulkin Muhammadu Buhari (daga 2015 zuwa 2023).

Wadannan bayanai na kunshe cikin littafin, ‘The Shadow Of Loot and Loss – Uncobering Nigeria’s Petrol Subsidy Fraud,’ wanda tsohon sarkin yaki da cin hanci da rashawa ya rubuta.

Alkaluman da Bawa ya bayyana daga cikin gwamnatocin hudu, shugaba Buhari ne ke kan gaba wajen biyan tallafin da ake ta cece-kuce akai na Naira tiriliyan 11, sai kuma na Jonathan wanda ya kashe Naira tiriliyan 3.9. Gwamnatin Obasanjo ta zo na uku da Naira biliyan 812 yayin da ‘Yar’aduwa ke biye da Naira biliyan 794.

Obasanjo da Buhari sun shafe shekaru takwas suna mulki yayin da Jonathan ya yi mulki na tsawon shekaru shida, tun da farko ya kammala shekaru biyu da gwamnatin Yar’adua ta bari, a matsayin mataimakin marigayin, inda ya lashe zaben shugaban kasa a shekarar 2011.

A cikin littafin mai shafuka 317, Bawa ya ce kudaden tallafin, wadanda galibi na yaudara ne, ana samun su ne ta hanyar rashin isassun tsare-tsare, raunin tsarin aiwatar da doka, da kuma rashin gaskiya a cikin dukkan tsarin.

Bawa ya ce wadannan kura-kurai sun karfafa karuwar kudaden tallafin daga Naira biliyan 123 a shekarar 2006 zuwa Naira biliyan 886 a shekarar 2014 da kuma mummunan adadi na Naira tiriliyan 11 a shekarar 2023.

Tsohon shugaban na EFCC ya ci gaba da cewa za’a iya bayyana badakalar tallafin man fetur ta Nijeriya ta hanyar amfani da triangle na zamba na “Tsarin (Needs), Opportunity and Rationalisation.”

Ya ce, “Matsi shi ne abin da zai sa mutum ya yi zamba, samun dama kuma ita ce ke bayar da yanayin da mutum zai aikata zambar.

 

Yadda Aka Aiwatar Da Badakalar

Bawa ya gano hauhawar farashin shigo da kayayyaki, da sauya lokacin daftarin kaya, rashin bayyana dawo da kayan da aka shigo da su ta sama da kasa, da jirgin ruwa mai yawo, shigo da kaya guda daya, tare da biyan tallafi a kansa sau biyu, na daga cikin hanyoyin da aka tafka badakalar tallafin man fetur.

A cewarsa, kamfanonin sayar da man sun yi amfani da yawan shigo da kayayyaki don kara yawan kudaden tallafi daga karshen shekarun 2010.

Ya ce binciken da aka gudanar ya sa hukumar EFCC ta gano haramtattun kudaden da suka haura Naira biliyan 30.

Bawa ya ci gaba da cewa, “A lokuta da dama, an samu jami’an gwamnati da saninsu ko kuma ba da saninsu ba, ta hanyar buga tambari da sanya hannu a cikin takardun jabun, wasu jami’an sun ce sun sanya hannu a kan takardun a lokacin da suke bakin aiki, duk da cewa suna sane da cewa lamarin ba haka yake ba, akwai wadanda suka sanya hannu kan takardun bogi, ba tare da sanin cewa an kirkiresu ba ne.

Ya ba da misali da yadda wani kamfani ya shigo da lita miliyan biyar kasa da mai fiye da lita miliyan 12. An biya kamfanin tallafin Naira miliyan 700, wanda bai cancanta ba.”

Wannan a cewarsa lamari ya ci gaba da haifar da tambayoyi masu mahimmanci game da hanyoyin damfara, gazawar sa ido na hukumomi, da kuma yadda EFCC ta gano wadannan haramtattun ayyuka.

 

Hanyar Kawo Karshen Lamarin

Dangane da kokarin hukumar na duba matsalar, Bawa ya ba da tarihin bincike, kamawa, tuhume-tuhume, yanke hukunci da kwato haramtattun dukiyoyi da hukumar ta yi.

Ya ce duk da cewa ba a samu wasu laifuka ba a shekarar 2006 da 2007, hukumar ta kwato Naira biliyan 11.5 a shekarar 2008, Naira biliyan 4.88 a shekarar 2009, da kuma Naira biliyan 10.3 a shekarar 2010.

Tsohon shugaban hukumar ta EFCC ya bayyana wata badakala da aka yi a 2011 ta tallafin man fetur, “a lokacin ne muka gano wasu haramtattum ayyukan da suka kai Naira biliyan 41.7.

“A dunkule, ayyukan damfara sun kai kusan Naira biliyan 68, wanda kusan kashi 80 cikin 100 an kwato su,” in ji shi.

Bawa ya kara da cewa, a cikin shekaru 25 na mulkin dimokuradiyya, Nijeriya ta kashe Naira tiriliyan 16.5 wajen bayar da tallafi, inda ya kara da cewa abin da ke daure kai ga daukacin al’amura shi ne yadda aka kashe kaso daga cikin kudaden wajen yin ikirarin karya da satar dukiyar kasa.

 

Hanyar Samun Ci Gaba

Bawa ya yi nuni da cewa, shi tallafin a kansa ba wani sharri ba ne; amma duk da haka, aiwatar da aikinta na yaudara ya sa gwamnati ta ki amincewa da dimbin albarkatun da aka tanada domin samar da ababen more rayuwa, inganta harkokin ilimi da kiwon lafiya, wadanda ke amfanar da marasa galihu a Nijeriya.

Don haka ya yi kira da a samar da ingantaccen tsarin bayar da tallafi.

Ya ce, “Kiyaye tsarin tallafin da aka sarrafa da kyau zai iya ba da agajin da ake bukata ga masu rauni ta hanyar tabbatar da cewa an dakatar da tsadar rayuwa, sannan gwamnatin ta tsaya tsayin daka wajen samar da wani abin dogaro ga matsalolin tattalin arziki.

“Wannan yana jaddada muhimmancin samar da ingantattun hanyoyin sa ido da daidaita yadda ake raba tallafin don hana cin zarafi da tabbatar da sun cika manufarsu.”

Bawa ya kuma yi kira da a ji tsoron Allah da gaske da kuma samar da ingantaccen tsarin adalci.

Bawa ya ce, “Tsarin ba wai kawai kayan ya ke ba wa kariya da kuma dakile laifuka ba, har ma ya mallakar karfin bincike da kuma hukunta laifukan da suka dace, yana da matukar muhimmanci, irin wannan tsarin na samar da amana da amincewa a tsakanin ‘yan kasa, tare da karfafa hadin gwiwar jama’a da kuma tabbatar da doka da oda.”

Tsohon shugaban na EFCC ya bukaci ‘yan Nijeriya da na kasashen waje da su canja halayensu, su bi ka’idojin da’a, su sanya al’ummar kasa a zuciyarsu sama da kansu.

Bugu da kari, ya yi kira da a samar da isassun kudade tare da tura fasahar kere-kere a cibiyoyin gwamnati domin dakile cin hanci da rashawa.

“Su koma al’adar yin abin da ya dace, ba tare da la’akari da yanayin ba, hakan na iya haifar da sauye-sauye masu dorewa a cikin al’amuran al’umma,” in ji shi.

LEADERSHIP Sunday ta ruwaito cewa an samu wasu ‘yan Nijeriya da dama da laifin zamba a cikin tallafin man fetur, na baya-bayan nan shi ne Mamman Ali, dan Ahmadu Ali, tsohon shugaban jam’iyyar PDP mai mulki a lokacin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Naira tiriliyan Naira biliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan Almutaba (a) 120

120-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da haka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissoshin da suka zo cikin alkur’ani mai girma ko kuma cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin Dastane Rastan na Aya. Shahid Murtadha Muttahhari, ko kuma cikin littafin mathnawa na maulana Jalaluddeen Rum ko kuma cikin wasu littafan da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu.

////… Madallah, masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata a kuma cikin sarir Imam Al-Hassan Almujtaba (a) diyar Fatima (s) kuma jikan manzon All..(s) na farko , mon tsaya inda muka bayyana yadda Talha da Zubair suka bukaci Amirulmuminina (a) ya yi masu izini su je umra amma sai ya dubesu da idon shakka, sai yace masu ba umra kukeson zuwa ba. Kuna son yaudara ne. kuna son kwance bai’ar da kuka yi mani. Sai suka sake rantsewa kan cewa umra suke son zuwa. Sai ya sake karbar bai;a daga wajensu. Don ya tabbatar masu shifan da manzon All..(s) ya fada masa, dangane da su. Inda yake fadawa Imam Aliyu dan abitalib (a) kan cewa: Zaka yaki, a bayana,  masu kwace alkawali, da azzalumai da kuma wadanda suke saurin ficewa daga addini” Kamar yadda ibn Abil hadida ya kawo a cikin littafinsa sharhin Nahjul Balagha, JZ 1,  shafi na 201.

Sai kamar yadda zamu gani a nan gaba, da Talha da Zubai, da A’isha matar manzon All…(s) sun daga cikin wadanda suka kasance masu karya alkawali, wadanda manzon All.. (s) yace Aliyu zai yake su.

Daga nan sai ya barsu suka fita zuwa Makka. Inda suka je suka sami cewa Aisha tana cikin bakin ciki a lokacinda ta ji labarin cewa Aliyu dan abitalib (a) ya zama khalifa a bayan kissan Khalifa Uthman.

Malaman tarihi sun bayyana cewa bayan an kammala aikin Hajji na wancan shekarar,  sai ta kama hanyar Madina daga Makka, tana sauri don ta je da ga abinda Zai faru da Khalifa Uthman.

Malaman tarihin sun bayyana cewa, Aisha tana daga cikin wadanda suke ingiza mutane, kan khalifa Uthman. Wasu sunce ta fara sabani da shi ne tun lokacinda, ya haw kan kujerar Khalifanci, sai ya daidaita ta da sauran matan manzon All..(s) a rabonsu na dukiya da khalifa Umar yake basu.

Khalifa Umar yana fifitata a kan sauran matan manzon All..(s) amma Khalifa Uthman ya dai-daitasu da ita.

Wannan daya Kenan, sannan wata rana ta je wajensa tace ya bata gadonta, daga manzon All..(s). Sai yace mata, wani gado kuma, kina daga cikin wadanda suka shaida kan cewa: manzon All..(s) yace: Mu annabawa ba’a gadommu, abinda muka bari sadaka ne) a lokacinda Zahra (s) ta nemi gadonta daga babanta, kun hanata gadon babanta, sannan ki zo kice a baki gadonki daga manzon All..(s). sai ya hanata ta kara fushe da shi. Tun lokacin sunansa a wajenta ya zama Nathal, wato mai yawan gashi a jiki. Don haka basa shiri da ita.

Sannan ta bar Madina ta kama hanya zuwa Hajji a dai dai lokacinda yan tawaye suka yiwa gidan Khalifa kawanya.

Don haka da ta kammala aikin hajji sai tana sauri zuwa Madina don ta ga abinda zai faru da shi.

Amma a lokacinda ta isa wani wuri da ake kira ‘Sarf’ da sini ko sharaf da shini, sunan wani wuri kimani mel 6 daga Makka, sai ta hadu da wani mutum, daga cikin dangin mahaifiyarta, wanda ake kiransa Ubaidullahi dan Salamah, wanda ya fito daga Madina, sai ta yi sauri ta tambaye shi, wani labari kake da shi daga Madina, sai ya ce mata: An kashe Uthman :

Sai tace, sannan sun yi me? Sai ya ce, sun gamu a kan bai’a ga Aliyu, sai al-amura suka zama alkhairi a garesu.

Sai jikinta ya mutu, yanayinta ya canzu tana daga kanta sama ta sake dawo da shi kasa, tana cewa: Wallahi, ina da ace wannan(sama) ta fadi ta hadu da wannan(kasa), idan har wannan al-amarin ya tabba ga dan abitalib, to an kashe Uthman a matsayin wanda aka zalunta, kuma zan nemi fansar jininsa.

Sai Ubaidullah, yace me ya sa? Na rantse da All.. mutum na farko wanda ya fara mummunan kalma a kansa ke ce! Kin kasance kina cewa: ku kashe Naathal ya kafirta.

Amma me ya sa Aisha take wannan bakin ciki mai tsananin, kan dawowar khalifanci ga Amirulmuminina (a)? ba kome ba musulunci ya dawo da karfinsa na farko da ya rasa tare da hukumar Aliyu dan abitalib (a). Musulmi sun sami abinda suka dade suna nema.

Amma sai Aisha ta amsa wa dan kawunta kan cewa, sun nemi uthman ya tuba, bayan ya tuba suka kashe shi.

A bin tambaya ita ce, shin tana nan a lokacinda haka ya faru? Tana nan a lokacinda suka bukaci khalifa Uthman tuba, kuma tana nan sannan ya tuba? Kuma tanan nan sanda aka kashe shi? Da wa da wa suka kasashe shi? Shin Amirul muminina (a) yana daga cikin wadanda suka bada umurni a kasashe? Idan ba haka ba, me ya sa za’a dora masa laifin kissan Uthman a lokacinda mutane suka zabe shi.

Duk wadan nan tambayoyi sai ta amsa su kafin ta ce, ya zama wajibi a gareta neman fansar jinin Khalifa Uthman da yakar gwamnatin Imam Ali (a).

Ga wanda yake son sanin menene tsakanin Amirulmuminina (a) da kuma Aisha matar manzon All..(s) da kuma abinda ya sa bata son ganinsa a matsayin khalifan musulmi ta ya koma yadda tayi da manzon All..(s) da kuma iyalan gidansa tsarkaka.

Na’am, wanda ya koma baya zai ga cewa ta yi amfani da neman fansar jinin Uthman don yakar Amirulmuminina (a) ne don tsohuwar gaba da kiyayyar da takewa wannan gidan mai tsarki tun manzon All..(s) yana da ransa.

Aisha matan manzon All..(s) bata son wani alkhairi gad an uwan manzon All…(s) kuma ma’ajiyar ilminsa da matarsa diyar manzon All..(a) da kuma yayansu Alhassan da Alhussain (a) tun manzon All..(s) yana da ransa. Ta ga yadda manzon All..(s) yake girmamasu, yake, ya kebesu da kebebbiyar sonsa a garesu, ba don su danginsa ne ko kuma dan amminsa da diyarsa da jikokinsa bane, ee shi haka ne a garesu, amma don matsayin da suke da shi a wajen All..mai girma da daukka, Aliyu wasiyyinsa ne, tare da zaben All..T, ba babanta ba, Fatimah (s) diyarsa ne, amma kuma All…ya sanyata shugaban matan Aljanna, na duniya da lahira. Sannan Alhassan da Al-husain jikokinsa ne, amma kuma All…ya sanyasu cikin wasiyyan manzon All…(s) kuma daga tsotson Hussainine sauran wasiyansa 9 zasu fito. Na karshensu shi ne Mahdi na wannan al-ummar.

Don wadannan matsayi da daukakan da All..yayi masu ne suka gamu da hasadan masu hasada.

Wata rana manzon All.. (s) yana khudaba a cikin masallaci, sai yayi ishara da hannunsa ga dakinta, yana cewa,: Nanne fitina, nan ne fitina, nan ne fitina daga inda kahon shaitan zai fito.

Wannan kamar yadda ya zo a cikin Shahihul Buhari JZ daya, shafi na 125 a babin wajibcin Khumusi,

Hadisi mai kama da wannan ya zo a cikin Sahih Muslimu JZ na biyu  shafi na 503

Malaman tarihi sun bayyana cewa manzon All..9s) ya yi mata barazana da sakinta sau da dama, saboda yadda take cutar da shi da wadannan iyalan gidansa tsarkaka.

Ta ga yadda manzon All..(s) ya himmato da sin Aliyu da Matarsa Fatimah (s), himmatuwar da dukkan matansa basu samu irinsa ba.   

Wata rana babanta ya nemi izinin shiga wajen manzon All..(s), a lokacinda ya shiga, sai ya ji muryanta sama da muryar manzon All..(s). tana cewa: Wallah na san cewa, Aliyu ya fi soyuwa a wajenda da ni da babana, ..ta nanata wannan har sau biyu ko uku.

Kamar yadda Ahmad bin Hambal ya kawo a cikin Musnadinsa JZ 4 shafi na 275.

Banda haka, wani abinda yake mata zafi shi, bata haihuba, kamar yadda sauran matansa basu haihu ba, amma sai tana ganin yadda ya maida soyayyansa da jikokinsa Imam Hassan da Imam Alhussain. Yana sonsu matukar so, baya son duk abinda zai taba su.

Don haka ta tsaya tsayin daka, tun bayan manzon All..(s) don tabbatar da cewa Alioyu bai sami matsayin khalifanci ba. Amma gashi al-amarin ya kubuce mata. Ali ya zama Khalifa. Shi ne take neman duk wata hanya ta fidda khalifanci daga hannunsa.

Wannan duk tare da cewa ta ji manzon All..(s) yana fada dangane da Aliyu (a) falaloli, masu yawa. Cewa shi danuwansa ne, matsayinsa da shi, kamar matsayin haruna da Musa ne, har ya kara da cewa a hadisin Ghadir: Ya ubangiji ka jibanci wanda ya jibanceshi ka yi adawa da wanda yayi adawa da shi ka tabard wannan ya tabar da shi, ka risker da gaskiya tare da shi.) har zuwa karshen hadisin.

Amma hasada da rufe zuciyarta, tana neman duk wata hanya ta yakarsa da kuma dauke khalifanci daga hannunsa idan zata iya.

Sannan wani abnda ya sa bata son khalifanci ga Aliyu dan Abitalib sun hada da cewa tana son khalifanci ta koma cikin danginta, Banu taim. Tana son dan amminta Talha dan Ubaidullah ya zama Khalifa. Kamar yadda wasu malaman tarihi, musamman Akkad ya kawo a cikin littafinsa mai suna Abkariyyatul Imam Ali (a).

Hakama Ibnu Abil hadid ya kawo shi cikin sharhinsa na Nahjul Balagha JZ 6 shafi na 215.

Sannan na uku, wasu malaman tarihi suna ganin, ta fake ne da neman jinin Uthman, amma a shari’a, mai neman jinin wanda aka kashe shi danginsa na kusa, musamman dansa na cikinsa, idan babu shi to shugaban musulmi shi ne da hakkin ya nemi jinin wanda bai da waliyi. Khalifa Uthman yana da yaya maza wadanda zasu nemi hakkin zubar da jinin mahaifinsu, Aisha da Talha da Zubair da Mu’awiya da sauransu basu da hakkin neman jinin Uthman a lokacinda yayansa suna da rai. Sannan khalifan musulmi yana nan.

Wannan babban malami Allamah Ala’ili dan kasar Lebanon amma yayi karatu a jami’an alazhar a cikin littafinsa.

Masu sauraro a nan zamu dasa aya a cikin shirimmu nay au sai kuma wata fitowa idan All..ya kaimu assalamu alaikum wa rahamatullahi wa barakatuhu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar
  • Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021
  • Gwamna Namadi Ya Biya Sama Da Naira Biliyan Daya Ga Tsofaffin Ma’aikata
  • Matawalle Ya Bada Tallafin Kudi Da Kayayyakin Abinci Ga Iyalan Marigayi Sarkin Gusau
  • Kissoshin Kayuwa: Sirar Imam Hassan(a) 122
  • Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Hassan Almutaba (a) 120
  • IRGC Ta Ja Kunnen Kasashen Turai Dangane Da Taimakon Da Suke Bawa HKI
  • LP za ta ceto Nijeriya daga halin da APC ta jefa ta — Nenadi Usman
  • Tallafin Lafiya: Ƙungiyar Rotary Ta Raba Kayan Haihuwa kyauta Ga Mata Masu Juna Biyu  A Kaduna
  • NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159