Muhimmanci, Tasiri Da Kuma Amfanin Jigida Ga Mata
Published: 14th, June 2025 GMT
Ita jigida irin ta da ba haka kawai ake sakata ba, domin shahararru kuma jarumai ne a wacan lokacin suke yin ta don haka ne take da tasiri da kuma tsada ga masu saye.
Sai dai a baya akwai jigida ta ‘yan mata akwai ta matan aure da kuma na tsofaffi, kuma a wannan lokacin babu matsala ko wani gani-gani da ake yi wa macen da aka ganta sanye da jigida saboda abu ne da aka dauka na al’ada maimakon ado ko kiran maza da wasu ke ganin matan yanzu suke yi da jigida ba.
Yanzu dai sanya jigida ga mata ya bunkasa ya fadada har cikin kashen Turai. Matan turawa kamar yadda bincike ya tabbatar kashi 60 cikin 100 suna sawa.
Sai dai a wannan zamanin da muke ciki sanya jigida ga mata ya zama abin ado ne ba domin dalilai irin na camfi da muka ambata a baya da mutanen baya suke yi ba, duk da yake ana samun kadan daga cikin matan kauyawa masu saka jigida da manufa ta camfi.
Shima dai kamar irin na da ne, wannan zamanin ana yin jigida ne da wasu duwatsu masu kyalli da kuma robobi masu sheki wadanda nauyinsu bai kai irin na zamanin baya ba.
Babban alfanun da jigida yake yi wa mata kamar yadda bincike ya tabbatar a wannan lokacin shi ne, yana kara wa mace fadin kugunta ga irin matan nan da suke da karancisa.
Maza da dama da aka zanta da su sun nuna sha’awarsu ta ganin matansu na aure suna saka jigida domin yana karamusu kyau musamman idan mace tana sanye da kayan da za su bayyanasu.
Har ilayau cikin alfanun da jigida ke da shi shi ne ta kan motsa sha’awan maza a yayin da suka ji sautinsa ko suka hango shatinsa.
Sai dai duk da wadannan tasiri, mahimanci da alfanun da jigida ke da su ba duka mata bane suke sanyawa ba, haka ma maza da dama ba su son ganin mace da jigida. Wasu mutane sun riga sun kudura cewa duk mace ko budurwar da aka ga tana sa jigida ko aka ji sautinsa a tare da ita suna daukan irin wadannan matan mazinata ne.
Sannan kuma yanzu ana jigida ta mganin mata. Masu maganin mata sun samo yadda ake jigida da garin magani a maimakon duwatsun da ake yi da shi, sai a yi da maganin a ciccura ta kamar dutse sai a huda tsakiyar asa zare duk haka za’a jera su. Mata su daurashi a kugunsu yana maganin mata.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya yabawa Hukumar Makarantun Kimiyya da Fasaha ta Jiha bisa ƙirƙirar Kyautar Malami Mafi Nagarta, yana mai bayyana hakan da ɗaya daga cikin manyan manufofin da za su ƙarfafa koyo da koyarwa a fadin jihar.
A cikin wata sanarwa da Babban Jami’in Yaɗa Labaran sa, Hamisu Mohammed Gumel, ya fitar, gwamnan ya bayyana cewa bikin na farko na bada lambar yabo da aka gudanar a Dutse ya dace domin girmama malamai da suka yi fice ta hanyar jajircewa da sadaukar da kai.
Ya ƙara da cewa wannan mataki zai ƙara kwarin gwiwa, ya samar da gasa mai kyau, tare da inganta darussa a makarantu.
Namadi ya jaddada cewa ingancin ilimi bai tsaya kan gina makarantu kawai ba, yana ta’allaka ne ga ingancin malamai, kayan koyarwa da kuma yanayin makarantu.
Ya bayyana cewa gwamnatinsa ta fara ɗaukar malamai tare da horas da su akai-akai domin rage cunkoson ɗalibai da malamai da kuma horar da su sabbin dabarun koyarwa.
“Wannan shiri ɗaya ne daga cikin mafi kyawu da muka gani. Idan wani ya yi kuskure, sai a hukunta shi, yayin da duk wanda ya yi fice, wajibi ne a yaba masa. Wannan shi ne yadda ake samun cigaba,” in ji gwamnan.
Ya bukaci sauran hukumomin ilimi kamar Hukumar Gudanar da Makarantun Sakandare, Hukumar Ilimin Addinin Musulunci, da Ma’aikatar Ilimin Firamare su yi koyi da wannan tsari domin ƙara ƙarfafa gwanintar malamai a dukkan matakai.
Gwamnan ya kuma sake jaddada cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da maida hankali wajen gina makarantu, horar da malamai, da walwalar su.
Ya tabbatar da cewa za a ci gaba da baiwa bangaren ilimi goyon baya don inganta sakamakon koyo a makarantu a fadin Jihar Jigawa.
Usman Muhammad Zaria