Aminiya:
2025-06-14@09:32:34 GMT

An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia

Published: 13th, June 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan ƙasar Australia ta kama wata ’yar asalin Najeriya da ke ƙasar Australia, Binta Abubakar bisa zarginta da safarar ɗalibai daga ƙasar Papua New Guinea tare da tilasta musu yin aikin da ba a biya a gonaki a faɗin jihar Ƙueensland da sunan bayar da tallafin karatu.

Binta mai shekara 56, an kama ta ne a ranar Laraba a filin jirgin saman Brisbane a lokacin da ta isa ƙasar Papua New Guinea, inda take zaune.

Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8 Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi

Kamen nata ya biyo bayan wani bincike na tsawon shekaru biyu da ƙungiyar masu fataucin bil-Adama ta AFP ta yankin Arewa, wacce ta ƙaddamar da bincike kan ayyukanta a watan Yulin 2022 bayan samun bayanai daga ’yan sandan Ƙueensland.

A cewar AFP, “Wani gungun ‘yan asalin Papua New Guinea (PNG) da suka yi ƙaura zuwa Australia don yin karatu, an yi zargin cewa an tilasta musu yin aiki ba tare da son ransu ba a gonaki.”

An ba da rahoton cewa matar mai izinin zama ƙasashen biyu ta yaudari aƙalla ƴan ƙasar PNG 15, masu shekaru tsakanin 19 zuwa 35, zuwa Australia tsakanin Maris 2021 da Yuli 2023 ta hanyar kamfaninta, BIN Educational Serɓices and Consulting, da kuma ta hanyar ba da guraben karatu na bogi.

Rahoton ya bayyana cewa, shafin intanet na kamfaninta ya yi iƙirarin bayar da “daidaitaccen tsarin zamani don ilimi, horarwa da kuma aikin yi.”

Sai dai ’yan sandan sun ce gaskiyar lamarin ya sha bamban sosai.

Da zarar sun isa Australia, an yi zargin cewa an tilasta wa ɗaliban su sanya hannu kan jerin takaddun doka da ke tilasta su su biya kuɗin da ke da alaƙa da karatun, kuɗin jirgi, aikace-aikacen samar da biza, inshora da kuma kuɗaɗen doka.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Australia Safarar dalibai a Australia

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: June 12: Me Ranar Demokradiyya Ke Nufi Ga Talakan Najeriya?

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

An ayyana 12 ga watan Yunin kowace shekara a matsayin Ranar Dimokuradiyya a Najeriya don tunawa da ranar da aka gudanar da zaben da aka yi amanna cewa shi ne mafi sahihanci da inganci a tarihi.

Sai dai bayan fiye da shekara 30 da wannan zabe da fafutukar da ta biyo baya, wasu masana suna ganin har yanzu kwalliya ba ta biya kudin sabulu ba.

NAJERIYA A YAU: Hanyoyin Magance Matsalar Kwacen Waya

DAGA LARABA: Dalilan Rashin Jituwa Tsakanin Marasa Lafiya Da Jami’an Kiwon Lafiya

Ko mece ce hujjarsu? Wannan ne batun da shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung
  • Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi
  • Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje
  • NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya
  • 12 ga Yuni: Najeriya na bikin ranar dimokuraɗiyya
  • EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Zargi Aikata Damfara A Intanet A Kaduna
  • NAJERIYA A YAU: June 12: Me Ranar Demokradiyya Ke Nufi Ga Talakan Najeriya?
  • Na shirya yin haɗaka don ƙalubalantar Tinubu a 2027 – Amaechi
  • Tsohon Ɗalibi Ya Kai Hari Makarantarsu A Austria, Ya Kashe Ɗalibai 9