Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi
Published: 13th, June 2025 GMT
Rundunar Ƴanandan Jihar Bauchi ta kama wani matashi mai suna Umar Yau, wanda aka fi sani da “Snake,” bisa zargin damfara ta yanar gizo da satar bayanan wasu mutane. An kama Yau, mai shekaru 25 daga unguwar Yelwan Makaranta a Bauchi, bayan binciken da aka fara sakamakon ƙorafi daga wata mata da ya damfara.
Fatimah Faiz Ali Bawahab, wata ’yar kasuwa ta yanar gizo, ta kai ƙorafin cewa wani ya ƙirƙiri asusun bogi a Facebook da sunanta da hotunanta don damfarar mutane. CSP Ahmed Wakil, kakakin rundunar, ya ce wanda ake zargin ya ƙirƙiri asusun “Amizeebaby Muhd” inda ya ke tallata kasuwancin ƙarya, yana karɓar kuɗi daga mutane ta asusun banki.
Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi Mataimakin Firaministan Sin Ya Gana Da Ministar Kudin BirtaniyaAn gano cewa an taɓa damfarar wani Nafiu Muhd a watan Maris 2022, inda ya tura kudi zuwa asusun da ke dauke da suna Hansatu Yau, bayan haka aka toshe shi. Daga baya, bincike ya gano cewa ana amfani da sunayen Hansatu Yau da Umar Yau wajen karbar kuɗin jama’a a yanar gizo.
Bayan ƙorafin da aka samu, Kwamishinan ’Yansanda ya umurci gudanar da bincike na fasaha wanda ya kai ga kama Yau a ranar 5 ga Yuni, 2025. An kwato kati tara na ATM, katin zabe, na’urar MiFi, da sauran kayayyakin da suka tabbatar da laifin. Yau ya amsa cewa ya damfari mutane kusan 40 cikin shekaru biyar. An miƙa shi zuwa Rundunar ’Yansandan Kano don ci gaba da bincike da shari’a.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ambaliya ta yi ajalin mutane, ta lalata gidaje a Adamawa
Ambaliyar ruwa ta yi ajalin mutane da dama tare da lalata gidaje a Ƙananan Hukumomin Yola ta Arewa da ta Yola Kudu a Jihar Adamawa.
Ruwan sama mai ƙarfi da ya fara sauka tun da safiyar ranar Lahadi, ya haifar da ambaliya mai tsanani a sassan birnin.
An gabatar da kundin dokar hana cin zarafin mata a Gombe Rashin abinci mai gina jiki ya kashe yara 650 a Katsina — MSFYankunan da lamarin ya shafa sun haɗa da Yola Bye Pass, Sabon Pegi, Yolde Pate, da Modire.
Gidaje da dama sun nutse, gonaki sun lalace, hanyoyi kuma sun katse, lamarin da ya hana mutane da ababen hawa zirga-zirga.
Rahotanni sun nuna cewar mutane da dama sun rasu, ciki har da ƙananan yara.
Ya zuwa yanzu ba san adadin waɗanda suka rasu domin hukumomi na ci gaba da aikin ceto.
“Mutane da yawa sun rasu, musamman yara. Har yanzu muna kan aikin neman mutane. Ba mu taɓa tunanin hakan zai faru ba,” in ji Furera Adamu, wata mazauniyar Sabon Pegi.
Aminiya ta gano yankunan Shagari Low Cost da Sabon Pegi sun cika da ruwa gaba maƙil, wanda hakan ya tilasta wa mazauna yankin barin gidajensu domin neman mafaka a wasu wurare.
Ruwan bai tsaya baya ba har yanzu, wanda hakan zai sa da wuya a iya zama a ciki gidaje a yankin.
Tuni aka yanke wutar lantarki a wasu wuraren da ambaliyar ta fi shafa.
“Muka rasa komai,” in ji wani mazaunin Yola Bye Pass.
“Ruwan ya shigo ta yadda ba mu samu damar ɗebe kayanmu ba.”
Ruwan ya kuma shafe gonaki masu yawa, wanda ya haifar da tsoron za a iya fuskantar ƙarancin abinci a nan gaba.
Maigidanta da dama sun rabu da juna, sannan akwai hatsarin yaɗuwar cututtuka masu nasaba da ruwa sakamakon rashin tsafta a wuraren da ambaliyar ta shafa.
A lokacin haɗa wannan rahoto, Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Adamawa (ADSEMA), ba ta fitar da wata sanarwa ba tukuna.
Sai dai Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Adamawa, CP Dankombo Moris, ya tura ‘yan sanda yankin don taimaka wa mutane da ke cikin hatsari.
Wannan na cikin wata sanarwa da kakaki rundunar, SP Suleiman Yahaya Nguroje, ya fitar a ranar Lahadi.
“Ina mai tabbatar muku da cewa rundunar ‘yan sandan Jihar Adamawa tare da haɗin gwiwar sojoji da ke Yola sun tura jami’ai zuwa wuraren da abin ya shafa domin taimaka wa al’umma,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa an gano gawarwakin mutum biyu zuwa yanzu, kuma an kai su Asibitin Koyarwa na Jami’ar Modibbo Adama.