Leadership News Hausa:
2025-07-29@07:38:10 GMT

Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6

Published: 13th, June 2025 GMT

Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6

Gwamnatin Jihar Kano ta musanta zargin da wasu ke yi cewa ta karɓo sabon bashi na dala miliyan 6.6 daga watan Yuni zuwa Disamba 2023, tana mai cewa wannan zargi ƙarya ne marar tushe da aka ƙirƙira domin ɓata mata suna. Wannan na zuwa ne bayan wata ƙungiyar siyasa mai suna APC Patriotic Volunteers ta yi zargin cewa gwamnatin NNPP mai ci a jihar ta karɓo bashi daga ƙasashen waje ba tare da bayyana hakan ba.

Darakta Janar na Ofishin Gudanar da Basussuka a jihar, Dr. Hamisu Sadi Ali, ya bayyana cewa tun daga lokacin da gwamnatin Abba Kabir Yusuf ta hau mulki, ba ta karɓi wani sabon bashi ko na gida ko na waje ba, balle a ɓoye shi daga idon jama’a. Ya ce duk wani bashi da gwamnatin jihar ke aiki da shi a halin yanzu an gada ne daga gwamnatin da ta gabata.

Kocin Kano Pillars Usman Abdullahi Ya Ajiye Aikinsa Sarki Sanusi II Ya Yi Hawa Duk Da Umarnin ‘Yansanda Na Haramta Hawan Sallah A Kano

Dr. Ali ya kuma ƙalubalanci tsohon Sakataren Gwamnatin Jiha, Alhaji Usman Alhaji, wanda ya jagoranci ƙungiyar da ta yi zargin, yana mai cewa duk wanda ke da hujjar wannan zargi ya fito da takardun da ke tabbatar da hakan – ciki har da sunan mai bayar da bashin, kwafen yarjejeniyar, dalilin karɓa, da tsarin biyan bashin.

A cewarsa, akwai doka mai ƙarfi da ke kula da basussuka a jihar, wadda gwamnatin APC ta gabata ta kafa a 2021. Wannan doka ta bai wa ofishinsa ikon karɓar bashi cikin tsarin doka da cikakken sahihanci, kuma ba wani bashi da aka karɓa tun bayan 2023. Ya ce gwamnati na gudanar da harkokinta cikin gaskiya da rikon amana, kuma ba za ta lamunci ƙarya da siyasar ɓatanci ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

DR Congo: M23 Ta Yi Barazanar Kauracewa Sulhu da Gwamnatin Kongo

Kungiyar yan tawaye M23 wacce take iko da yanki mai yawa a gabacin Democradiyyar Kongo ta bada sanarwan cewa idan gwamnatinn kasar Kongo bada gaggauta sakin fursinonin kungiyar ba, to tana iya kauracewa tattaunawan da za’a gudanar a birnin Doha na kasar Qatar a watan mai zuwa.

Shafin yanar gizo na Africanews ya nakalto babban sakataren kungiyar kuma mai magana da yawunta yana fadar haka a ranar jumma’a.

Ya kuma kara da cewa bayan da kowa ya bayyana matsayinsa a wata mai zuwa ne ake saran bangarorin biyu wato gwamnatin kongo da kuma kungiyar M23 zasu rattaba hannu a kan yarjeniyar sulhu na gaskiya.

Ya ce tattaunawa da kuma amincewa da wasu ka’idoji wanda bangarorin biyu suka rattabawa hannu a watan da ya wuce a doha, sharer fage ne na yarjeniyar da za’a rattabawa hannu a ranar 18 ga watan Augusta mai zuwa a birnin Doha na kasar Qatar.  Benjamin Mbonimpa ya jaddada cewa a cikin alkawalin da suka dauka a taron Doha na farko shi ne a saki fursinonin M23 kafin taro nag aba, don haka idan an ki yin haka tabbas ba zamu je taro na gabata.

A halinn yanzu dai kungiyar M23 suna iko da mafi yawan lardin kivu na gabacin kasar Kongo.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Yusuf Ya Kafa Kwamitin Bincike Kan Mutumin Da Ake Tuhuma Da Safarar Miyagun Kwayoyi
  • Amurka Ta Dakatar Da Bai Wa ‘Yan Kasar Nijar Bisa Shiga Cikin Kasarta
  • Za A Fara Bayar Da Bashin Miliyan 10 Ga Ma’aikatan Manyan Makarantu
  • Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya
  • Gwamnatin APC ta jefa ’yan Najeriya cikin ƙangin talauci — Shugabar LP
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Kaddamar Da Dashen Itatuwa Na Bana
  • DR Congo: M23 Ta Yi Barazanar Kauracewa Sulhu da Gwamnatin Kongo
  • Gwamnatin Tarayya Ba Ta Soke Jarabawar WAEC Da NECO Ba
  • NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159
  • Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4