HausaTv:
2025-06-14@00:19:43 GMT

Sakon Jagora : Isra’ila ta jira hukunci mai tsanani bayan hari kan Iran

Published: 13th, June 2025 GMT

Bayan harin da gwamnatin Sahayoniya ta kai kasarmu, Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya aike da sako ga al’ummar Iran. Ga sakon kamar haka

Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai

Al’ummar Iran masu daraja!

Gwamnatin yahudawan sahyoniya ta hanyar aikata wani laifi da sanyin safiyar yau, ta sake bayyana munanan dabi’arta da fasadi.

Ta hanyar kai hari dole ne wannan ya fuskanci hukunci mai tsanani.

A wannan harin makiya, kwamandoji da masana kimiyya da dama sun yi shahada.

Wadanda suka gaje su kuma da abokan aikinsu za su ci gaba da aiki nan take akan wannan tafarki, godiya ta tabbata ga Allah.

Ta hanyar wannan danyen aiki, gwamnatin Sahayoniya ta kaddara akan ta cewa zata fuskanci martini mai radadi.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jagora Ya Bambance Tsakanin Majalisun Dokokin Kasashe A Fagen Gudanar Da Ayyukan Kasa

Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa: Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran ta sha bamban da majalisun da ke goyon bayan masu goyon baya masu laifi misalin masu kisan gilla a Gaza

Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya jaddada a yau Laraba cewa: Matsayin majalisar shawarar Musulunci ta Jamhuriyar Musulunci ta Iran ya bambanta da kasashen duniya, kuma ya sha bamban da majalisar da ke goyon bayan zalunci, nuna wariya, banbance-banbancen ra’ayi da masu aikata laifuka irin su kisan gilla a Gaza.

Yayin ganawarsa da mambobin majalisar shawarar Musulunci a ranar Laraba, Jagora ya yi la’akari da cewa: Majalisun dokokin duniya suna da kamanceceniya ta fuskar nauyi doka. Duk da haka, ya jaddada cewa ma’auni na farko don kimanta taro shine ainihin nauyin su, watau, “manufofin su, alkiblar motsi, da matsayi.” Wannan shi ne ya sanya matsayin Majalisar Shawarar Musulunci ke da shi a duniya. A dabi’ance, ci gaba da wanzuwar wannan matsayi mai mahimmanci da daraja yana buƙatar yanayi da wajibai waɗanda dole ne membobin su kiyaye.

A farkon jawabin nasa, Ayatullah Khamenei ya bayyana Eid al-Ghadir a matsayin biki mai girma ga daukacin al’ummar musulmin duniya, mai cike da ilmin addinin Musulunci. Ya taya al’ummar Iran masu girma da alfahari murnar zagayowar wannan rana mai albarka, da kuma maulidin Imam Hadi (a.s). Ya dauki matakin shari’a na majalisun dokoki a kasashe na duniya a matsayin mai sanar da doka. Ya kara da cewa, “Dokar ita ce ainihin sharadi na zamantakewar bil’adama, kuma dokokin da tunani na gamayya da zababbun wakilan jama’a suka samar sun fi samun karbuwa da kima.” Jagoran ya yi nuni da cewa ma’auni na gaskiya na majalisu ya bambanta da juna, sabanin nauyinsu na shari’a. Ya ce, “Mataki da kimar majalisar da ta ginu a kan addini, wadda ta kunshi mutane masu tsoron Allah, masu gaskiya, ta mai da hankali kan adalci, da goyon bayan wadanda aka zalunta, da fuskantar azzalumai”.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran
  • Na’im Kassim: Harin HKI Akan Iran Ba Abinda Zai Jawo Mata Sai Kaskanci
  • Jagora: “Yan Sahayoniya Su Saurari Ukuba Mai Tsanani
  • Harin Isra’ila a kan Iran ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zama dar-dar
  • Rundinar IRGC, ta sanar da shahadar babban kwamandanta Manjo Janar Hossein Salami a harin ta’addancin Isra’ila
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje
  • Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran
  • Jagora Ya Bambance Tsakanin Majalisun Dokokin Kasashe A Fagen Gudanar Da Ayyukan Kasa
  • Rikicin Filato: An sake kone gidaje 96 a Mangu