Rahoto: Hare-haren jiragen yaki marasa matuka sun kashe daruruwan fararen hula a Afirka
Published: 11th, March 2025 GMT
Kimanin fararen hula 1,000 ne aka kashe tare da jikkata wasu daruruwa a hare-haren jiragen yaki marasa matuki a nahiyar Afirka, yayin da ake ci gaba da yin amfani da jirage marasa matuka a nahiyar.
A cewar jaridar The Guardian, masu sharhi da nazari na cewa , daga shekara ta 2021 zuwa 2024, jami’an tsaro a kasashe daban-daban na nahiyar Afirka sun yi amfani da jiragen yaki marasa matuka wajen kai hare-hare, wanda kuma sau tari ana kashe fararen hula ne, maimakon masu aikata laifuka.
Dole ne wannan ya kawo karshe, kuma dole ne kasashen duniya su dauki matakai da suka dace waje saka kaidoji kan amfani da jiragen yaki marasa matuka, domin rashin yin hakan zai ci gaba da yin sanadin salwantar rayukan fararen hula da basu bas u gani ba, in ji Cora Morris, jami’a a cibiyar sanya ido kan amfani da makamai ba bisa ka’ida ba da ke da mazauni a Burtaniya..
An tabbatar da cewa jirage marasa matuka masu dauke da makamai sun kashe fararen hula a kasashen Afirka masu yawa sakamakon tashe-tashen hankula, da hakan ya hada da kasashen Sudan, Somalia, Nigeria, Mali, Burkina Faso, da Habasha, inda akasarin hare-hare sun faruwa ne a wadannan yankuna.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: jiragen yaki marasa marasa matuka fararen hula
এছাড়াও পড়ুন:
Jagoran ‘Yan Democrat a Majalisar Dattawa: Trump Ba Shi da Ikon Kaddamar da Yaki Kan Venezuela
Jagoran ‘Yan Jam’iyyar Democrat na Majalisar Dattawa Chuck Schumer ya zargi Shugaban Amurka Donald Trump da shirya yaƙi a ɓoye a kan kasar Venezuela, yana mai jaddada cewa ikon ayyana yaƙi ya rataya ne kawai a kan Majalisa, kuma dan majalisar ya bayyana cewa zai gabatar da kuduri don hana tura sojojin Amurka yaki a Venezuela.
Schumer ya tabbatar da cewa Trump ba shi da ikon aika sojojin Amurka zuwa yaƙi ba tare da izinin Majalisa ba, yana mai bayyana cewa wannan ikon an keɓe shi ne ga Majalisa kaɗai.
A cikin wata sanarwa, Schumer ya zargi Trump da shirin yaƙi a ɓoye da Venezuela, yana mai gargadin cewa Majalisa za ta ɗauki mataki nan take don gabatar da kuduri zai hana hana tura sojojin Amurka zuwa wannan yaki da yake Shirin kaddamarwa.
Schumer ya ce mutanen Amurka ba sa son wani yaƙi da ba a san karshensa ba, ya ƙara da cewa duk wani mataki mai ƙarfi a kan Venezuela ba tare da amincewar majalisa ba zai zama babban kure da kuma sab awa doka.
A wani labarin kuma, Schumer ya bayyana cewa ya sami barazana ta imel, daga abin da ya kira “MAGA” ko kuma (Make America Great Again) wato gungun da ke mara baya ido rufe ga siyasar Trump, kuma ya tabbatar da cewa hukumomin tsaro a New York sun sanar da shi barazanar da aka yi lokuta daban-daban na dana bam a ofisoshinsa.
A ranar Asabar da ta gabata, shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da cewa za a rufe sararin samaniyar Venezuela da yankin da ke kewaye da ita gaba daya.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Najeriya: Matatar Dangote Za Ta Mika Tataccen Mai Lita Biliyan 1.5 A Watan Disamba December 2, 2025 Ramaphosa ya yi watsi da barazanar Trump na ware Afirka ta Kudu daga G20 December 2, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan (a) 165 December 1, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan 164 December 1, 2025 Baqaei: Amurka Ce Babbar Barazana Ga Zaman Lafiya Da Tsaro A Duniya December 1, 2025 Paparoma Leo Na 14 Yana Ziyarar Aiki Na Kwanaki 3 A Kasar Lebanon December 1, 2025 Kamaru: Madugun Adawa Ya Rasu A Gidan Kaso December 1, 2025 Tawagar ECOWAS Ta Bar Guinea – Bissau bayan da shugaban kasar yayi barazanar korarsu Da Karfi December 1, 2025 Yawan Yahudawan Da Suke Ficewa Daga HKI Sun Nininka Har Sau 100% December 1, 2025 Gaza: Fiye da Falasdinawa 350 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila tun bayan tsagaita wuta December 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci