Kimanin fararen hula 1,000 ne aka kashe tare da jikkata wasu daruruwa a hare-haren jiragen yaki marasa matuki a nahiyar Afirka, yayin da ake ci gaba da yin amfani da jirage marasa matuka a nahiyar.

A cewar jaridar The Guardian, masu sharhi da nazari na cewa , daga shekara ta 2021 zuwa 2024, jami’an tsaro a kasashe daban-daban na nahiyar Afirka sun yi amfani da jiragen yaki marasa matuka wajen kai hare-hare, wanda kuma sau tari ana kashe fararen hula ne, maimakon masu aikata laifuka.

Dole ne wannan ya kawo karshe, kuma dole ne kasashen duniya su dauki matakai da suka dace waje saka kaidoji kan amfani da jiragen yaki marasa matuka, domin rashin yin hakan zai ci gaba da yin sanadin salwantar rayukan fararen hula da basu bas u gani ba, in ji Cora Morris, jami’a a cibiyar sanya ido kan amfani da makamai ba bisa ka’ida ba da ke da mazauni a Burtaniya..

An tabbatar da cewa jirage marasa matuka masu dauke da makamai sun kashe fararen hula a kasashen Afirka masu yawa sakamakon tashe-tashen hankula, da hakan ya hada da kasashen  Sudan, Somalia, Nigeria, Mali, Burkina Faso, da Habasha, inda akasarin hare-hare sun faruwa ne a wadannan yankuna.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: jiragen yaki marasa marasa matuka fararen hula

এছাড়াও পড়ুন:

 Iraki: An Kashe Shugaban Kungiyar “Da’esh” Na Iraki Abdullahi Makki

A jiya juma’a ne dai firma ministan kasar Iraki Muhammad Shi’ya al-Sudani ya sanar da cewa sojojin kasar sun kashe babban dan ta’adda Abdullahi Makki wanda ake yi wa lakabi da Abu Hadiza.

Al-Sudani ya kara da cewa; Iraki taba cigaba da samun nasara akan ‘yan ta’adda, bayan da jami’an tsaro na kasa da kasa su ka yi nasarar kashe Abdullahi al-makki, wanda ya kasance a matsayin  mataimakin shugaban abind ake kira da Daular Musulunci a Iraki da Syria.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • MDD ta bukaci masu ruwa da tsaki a Yemen da su kai zuciya nesa
  • Yemen: Amurka Ta Sake Kai Wani Harin A Kasar Yemen
  • Adadin Shahidan Falasdinawa A Gaza Ya Karu Da 14 A Jiya Lahadi Saboda Hare-Haren Sojojin HKI
  • Kungiyar Ansarullah Ta Ce Keta Hurumin Kasar Da Amurka Ta Yi Zai Gamu Da Maida Martani
  • Kasar Habasha Ta Bukaci Kasashen Afirka Su Bunkasa Ciyar Yaki Da Cututtuka CDC Da Kungiyar
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 31, sun lalata sansaninsu a Katsina
  • Fiye Da Mutane 20 Ne Su Ka Yi Shahada Sanadiyyar Hare-haren  Amurka Da Birtaniya Akan Kasar Yemen
  • Kungiyoyin Falasdinawa Suna  Cigaba Da Yin Allawadai Da Hare-haren Amurka Da Birtaniya Akan Kasar Yemen
  •  Iraki: An Kashe Shugaban Kungiyar “Da’esh” Na Iraki Abdullahi Makki
  • Iran Ta Yi Tir Da HKI Da Kokarin Wanke Kanta Tare Da Rabawa Addinin Musulunci Ta’addanci