Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran
Published: 14th, June 2025 GMT
Farashin Man Fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin da Isra’ila ta kai wa Iran, lamarin da ya tayar da hankalin masu zuba jari.
Ana fargabar cewa rikicin da ke ƙara taɓarɓarewa tsakanin ƙasashen biyu zai iya kawo tangarɗa wajen samar da man fetur daga yankin Gabas ta Tsakiya.
An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8Wani muhimmin wurin da ake safarar man fetur na duniya, wato mashigar Hormuz da ke kusa da Iran na da matuƙar tasiri, domin kashi ɗaya cikin biyar na dukkanin man da ake fitarwa daga nan ne ake bi da shi.
Amma duk da haka, kasuwannin hannun jari sun fuskanci faɗuwar daraja saboda rashin tabbas da harin ya haifar.
Sai dai darajar wasu hajojin da ake ɗauka amintattu a lokutan rikicin irin su zinariya da kuɗin ƙasar Japan, Yen sun tashi sama, domin masu zuba jari na ƙoƙarin neman mafaka a cikinsu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: hari Iran Isra ila Tashin Farashi
এছাড়াও পড়ুন:
Harin Ta’addanci A Wani Coci Ya Lashe Rayukan Mutane Fiye Da 21 A Gabashin Kongo
Fiye da mutane 21 ne suka mutu a wani harin ta’addanci da aka kai kan wani coci a gabashin Kongo
Rahotonni sun tabbatar da cewa; Sama da mutane 21 ne aka kashe a wani hari da mayakan ‘yan tawayen kungiyar Allied Democratic Forces (ADF) suka kai kan wani cocin Katolika da ke gabashin Kongo, wanda ya hada da kona gidaje da shaguna a yankin.
A ranar Lahadin da ta gabata ne mayakan da suke da alaka da kungiyar Allied Democratic Forces (ADF) da ke samun goyon bayan kungiyar ‘yan ta’adda ta ISIS suka kaddamar da harin ta’addanci kan wata majami’ar Katolika a gabashin Kongo.
“Sama da mutane 21 ne aka kashe a ciki da wajen cocin,” Dieudonné Duranthabo, wani jami’in kungiyoyin farar hula a Komanda, ya shaidawa kamfanin dillacin labarai na Associated Press cewa: “Sun gano akalla gawarwakin mutane uku da suka kone, sannan an kona gidaje da dama.”
Harin ya faru ne da misalin karfe 1:00 na safiyar Lahadi a cikin wani cocin Katolika da ke yankin Komanda a gabashin Kongo. An kuma kona gidaje da shaguna da dama.