‘Yan Wasa Biyar Da Suka Taka Rawar Gani A Kofin Zakarun Turai
Published: 15th, June 2025 GMT
Sannan shi ne ya fi kowanne danwasa yunkurin cin kwallo a gasar, inda ya kai hari (attempt) sau 64, 23 daga cikinsu akwai munana (on target) 23.
Ya yi nasarar yanka abokan hamayyarsa har sau 62, sannan ya yi bugun kwana 45.
Rapinha
Zakakurin danwasan gaba na Barcelona da Brazil, Rapinha, na cikin ‘yanwasan da suka fi bai wa mabiya harkokin wasa mamaki a kakar wasa ta bana baki daya – ba a Champions League ba kawai.
Rapinha mai shekara 28 ya ci ƙwallo tara da ƙafarsa ta hagu, uku da dama, da kuma ɗaya da kansa. Huɗu daga cikin ƙwallayen da ya ci daga wajen yadi na 18 ne.
Wani abu da ya kamata a lura da shi shi ne babu bugun finareti ko ɗaya cikin ƙwallayen da ya ci a wasa 14 da ya buga.
Lamine Yamal
Duniya ta fara maganar dan wasa kuma matashin da ya fi birge ‘yankallo ko shakka babu shi ne Lamine Yamal na Barcelona. Dan wasan na Sifaniyan mai shekara 17 ya taka rawar gani cikin wasanni 13 da hya buga wa kungiyar, inda ya kai hare-hare har sau 52. Daga cikinsu akwai munana 25. Yamal ya ci kwallo biyar sannan ya bayar da uku aka zira a raga. Sannan ya yi nasarar yanka abokan hamayya har sau 109 a gasar, wadda ita ce ta biyu da ya buga wa Barcelona.
Serhou Guirassy
Shima dan wasa Serhou Guirassy wani danwasan da ya taka rawar gani a kakar da aka kammala shi ne Serhou Guirassy na Burossia Dortmund da kuma Faransa. Danwasan mai shekara 29 ya jefa kwallaye har 13 a raga – iri daya da na Rapinha – sannan ya bayar gudummawa aka ci wasu hudu cikin wasa 14. Cikin kwallayen da ya ci har da uku rigis ya dura wa Barcelona a wasa na biyu na zagayen kusa da na kusa da na karshe.
Harry Kane
Danwasan gaba na Bayern Munich kuma kyaftin ɗin Ingila ya ɗora kan abin da ya saba, inda bai gushe ba sai da ya zira kwallaye 11 cikin wasanni 13 da ya buga wa kungiyar, kazalika, Kane mai shekara 31 ya kai hare-hare 49, cikinsu akwai masu hadari 25. Haka nan, ya bayar da kwallo biyu an zira a raga kafin Inter Milan ta yi waje da su daga gasar a zagayen kusa da na karshe.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Serhou Guirassy mai shekara
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina
’Yan bindiga sun tarwatsa kauyaku sama da 10 da ke zagaye da ƙaramar hukumar Bakori ta jihar Katsina.
Maharan dai sun rika kashe mazauna kauyukan sannan su sace wasu su yi garkuwa da su domin karɓan kuɗin fansa.
Bayanai na cewa a ’yan kwanakin nan, ’yan bindigar na cin karensu babu babbaka a inda suka tarwatsa kauyuka kamar su Guga da Kandarawa da Kakumi da kuma Monono.
Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACF DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aureHar ila yau lamarin ya shafi ƙauyukan anguwar ’Yar Dabaru da anguwar Ɗan Marka, da Sabon Gida da ƙauyan Doma da dai sauran su.
Hakan dai ya haifar da kauracewa ƙauyukan ga mazaunansu da suke da sauran numfashi inda a yanzu haka ake da ’yan gudun hijira sama da 3,500 da ke neman mafaka a cikin garin Bakori.
Kazalika, rahotanni sun kuma ce akwai wasu sama da 2,500 da ke garin Guga don neman mafaka.
’Yan gudun hijirar wadanda akasarinsu mata ne da ƙananan yara sun watsu a wurare daban daban.
Aminiya ta zagaya unguwan Kafaɗi da unguwar Ma’aru da ke Sabuwar Abuja a cikin garin na Bakori, inda wakilinmu ya tarar da cincirindon mata da ƙananan yara a rakuɓe, a gidajen ’yan uwa, wasu kuma a makarantun firamaren gwamnati da ke karamar hukumar ta Bakori.
A tattaunawar Wakilinmu da wasu daga cikin ’yan gudun hijira wadanda suka fito daga kauyaku daban-daban na jihar, sun nuna alhininsu game da yadda ’yan bindigar ke cin karensu ba babbaka a yankin.
Imrana Shafi’u wanda ’yan bindigar suka harbe shi a ƙafa har wuri biyu, wanda shi ya yi hijira ne daga kauyan Ɗan Marka, ya ce lamarin na da ban tsoro matuƙa.
A cewarsa, “Ni ma Allah ne ya sa zan rayu domin ’yan bindigan sun zaci na mutu ne.
“Domin da suka zo kanmu harbin kan mai uwa da wabi, suka yi ta yi, inda suka kashe mutane da dama.
“Ni ma dai Allah ne ya tsirar dani, domin duk wadanda nake tare da su duk an kashe su, ni kadai na tsira cikin ikon Allah,” in ji shi.
Ita kuwa Malama Marawiya wacce ta yi gudun hijira daga kauyan ’Yar Dabaru ta ce da rana tsaka ’yan bindiga suka keto cikin kauyan nasu, suka tarwatsasu sa’ilin da suka tasa ƙeyar mata sama da 10 kuma duk yawancinsu suna ɗauke da goyo suka yi cikin daji da su.
Marawiya ta kara da cewa kusan kwanakin matan 10 ke nan a hannun su kuma sun ce sai an biya kudin fansa har Naira miliyan daya da rabi kan kowanne mutum daya kafin a sake su.
Ta Kara da cewa “A da in suka dauki mutum bai wuce su ce a ba su Naira dubu ɗari biyar ba amma a wannan karon sai suka ce sai an biya har sama da naira miliyan daya da rabi ga kowanne mutum,” in ji ta.
Yusuf Usman, wanda suka yi sansani a wata makarantar Firamare ta Nadabo da ke cikin garin Bakori, ya ce kusan su ɗari uku ne suka yi gudun hijira daga kauyan Doma, cikinsu har da tsofaffi.
Ya kuma ce, “A haka muka tako da ƙafa muka yini muna tafiya tare da mata da yaran kanana har Allah ya kawo mu garin Bakori,” in ji shi.
Ya kara da cewa kusan shekara biyar kenan suna fama da wannan matsalar ta tsaro, kuma ba dare ba rana bare damina ko rani, haka ake shigowa kauyakun su ana kashe su sannan kuma a tasa ƙeyar su a tafi da su daji domin karɓan kuɗin fansa.
Shugaban kwamitin da ƙaramar hukumar Bakori ta kafa domin kula da ’yan gudun hijirar, Mallam Mamman Yaro Bakori, ya ce adadin ’yan gudun hijirar sun kai 3,500 a garin Bakori.
Ya Kara da cewa a garin Guga Kuma akwai akalla kimanin mutane 2,500 da suke gudun hijira a can.
Shugaban ya ce kuma kusan a kullum yawan su ƙaruwa yake yi, sannan suna warwatse ne a wurare daban daban a inda wasu suke zaune a gidajen ‘yan uwansu wasu kuma suna zaune ne a makarantar firamare ta Nadabo a cikin garin Bakori.
Sai dai ya ce tuni Shugaban ƙaramar hukumar Bakori, Abubakar Barde ya bayar da umurnin kai masu tallafin kayan abinci sau uku a rana tare da kudin cefane don saukaka masu rayuwar da suke ciki.
Wasu na bayyana cewa a ‘yan kwanakinnan ’yan bindigar na cin karensu babu babbaka a inda suka kafa sansaninsu a dajin Guga da Kandarawa da Kakumi.