Ma’aikatar Gona da tsaron abinci ta ƙasa ta dakatar da shirinta na gudanar da addu’a da azumi na kwanaki uku, bayan martani mai zafi daga jama’a. Tun da farko, an tsara addu’ar ne domin neman taimakon Ubangiji wajen tabbatar da tsaron (wadataccen) abinci a Nijeriya.

Wata takarda da ta bayyana ga jama’a, wadda Daraktar Gudanarwa ta Ma’aikatar, Mrs.

Adedayo Modupe O., ta sanya wa hannu, ta gayyaci daraktoci da sauran manyan ma’aikata domin halartar wannan taron addu’a a shalƙwatar ma’aikatar a Abuja, a ranakun 16, 23 da 30 ga Yuni, 2025.

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Addu’ar Kwana 3 Don Samun Isasshen Abinci Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

Sai dai cikin wata sabuwar sanarwa daga wannan darakta, an bayyana cewa an dakatar da shirin addu’ar har sai wani lokaci na gaba, ba tare da bayyana dalilin janye umurnin ba. Wannan matakin ya biyo bayan suka da jama’a suka yi a kafafen sada zumunta kan dacewar shirin.

Masu sukar sun bayyana cewa gwamnati ya kamata ta mai da hankali wajen samar da tsare-tsare na zahiri kamar gyaran dabarun noma, da tallafawa manoma da kuma inganta rarraba abinci, maimakon dogaro da addu’a wajen shawo kan matsalar yunwa da hauhawar farashin abinci.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba November 2, 2025 Manyan Labarai 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su November 2, 2025 Manyan Labarai Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya November 2, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministar Jin Dadin Jama’a ta Sudan: Mayakan RSF Sun Kashe Mata 300 Da Yi Wa 25 Fyade A El Fasher
  • Majalisar Karamar Hukumar Bubura Ta Kai Tallafin Kayayyakin Abinci Cibiyar Gyaran Hali
  • Gumi Ya Nemi Nijeriya Ta Katse Hulɗa Da Amurka Idan Trump Bai Janye Barazanar Sa Ba
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka
  • Jamus ta shiga sahun ƙasashen da ke neman kawo ƙarshen yaƙin Sudan
  • Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar