A cewarsa, dukkanin takardar neman kirkirar sabon masarauta ko sarki ko gunduma dole ne a aike zuwa addireshin gwamnan jihar ta hannun babbar sakatariyar ma’aikatar kananan hukumomi da kula da masarautu na jihar.

Kazalika, ya ce dole ne masu nema su gabatar da takaitaccen tarihin al’ummar da suke nema wa masarauta ko sarki ko gudunmawa tare da tarihin masarautar ko sarki ko gundumar da ke yankin da suke neman fita daga ciki.

Sanarwar ta kuma nemi a sanya dukkanin wani muhimmin bayanin da aka san zai iya taimakawa wajen la’akari da bukatar masu nema.

Har ila yau, sanarwar ta ce dole ne a takardar neman a samu sahihin sanya hannun hakimi, sarakunam kauye, da shugabannin al’umma tare da tabbacin wannan neman ta fito ne daga al’ummar wannan yankin da ake nema mata masarauta ko sarki ko gunduma.

Sanarwar ta kara da cewa duk al’ummomin da ke son kirkirar sabbin masarautu, sarakuna, ko gundumomi su na da dama kuma su na da ‘yancin gabatar da bukatar neman.

Gidado ya jaddada cewa shirin na daya daga cikin kudirin gwamnati na bunkasa gudanar da harkokin kananan hukumomi, da kiyaye al’adu, da karfafa cibiyoyin gargajiya a matsayin muhimman ginshikan zaman lafiya, hadin kai, da ci gaba masu ma’ana.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: ko sarki ko

এছাড়াও পড়ুন:

 Shugaban Kasar Amurka Ya Siffata Masu Zanga-Zanga A Los Angeles Da Dabbobi

Shugaban kasar ta Amurka wanda ya gabatar da jawabi a gaban sojojin kasar a sansanin ‘Fort Bragg’ dake Jahar North Carolina ya  bayyana cewa; Jahar Los Angeles tana fuskantar mamaya daga makiya ‘yan kasashen waje.”

Har ila yau shugaban na Amurka ya ce; Ba za mu bari a rika kai wa jami’an tsaron gwamnatin tarayya hari ba, ba kuma za mu bari a mamaye wani gari daga cikin garuruwan Amurka ba.”

Shugaban kasar ta Amurka ya kuma ce; Abinda birnin  Los Angeles yake fuskanta hari ne daga kowace kusurwa da ‘yan daba suke yi, kuma suna dauke da tutocin kasashen waje.”

Birnin Los Angeles yana fuskantar gangami da Zanga-zanga saboda nuna kin amincewa da Shirin korar ‘yan ci-rani ba bisa ka’ida ba.

 An sami sabani da rashin jituwa a tsakanin gwamnatin tarayya da kuma ta jaha akan matakin da ya kamata a dauka domin magance matsalar bakin hauren.

Gwamnan Jahar ta Califonia ya zargi shugaban kasar Donald Tump da kama-karya saboda aikewa da sojoji akan titunan birnin domin fuskantar masu gangamin da Zanga-zangar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin
  • Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi
  • Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa
  • Gwamnatin Kano Ta Ƙaryata Karɓo Bashin Dala Miliyan 6.6
  • Iran ta caccaki kudurin IAEA wanda ta ce yana cike da siyasa
  • Ana shirin mayar da rantsar da Shugaban Nijeriya zauren majalisa
  • An kashe mutum 15 a sabbin hare-hare a Filato
  • Za a dauke wa jihohin Arewa maso Gabas wutar lantarki na tsawon kwana 4
  •  Shugaban Kasar Amurka Ya Siffata Masu Zanga-Zanga A Los Angeles Da Dabbobi