HausaTv:
2025-07-08@05:15:31 GMT

 Fiye Da  Falasdinawa 50 Ne Su Ka Yi Shahada A Yau Alhamis

Published: 22nd, May 2025 GMT

Ma’aikatar kiwon lafiya ta Gaza ta sanar da cewa; Daga safiyar yau Alhamis zuwa yanzu adadin falasdinawan da su ka yi shahada sun haura 50.

Kididdigar ma’aikatar kiwon lafiya ta Gaza ta bayyana cewa  a cikin sa’oi 24 da su ka wuce an kai shahidai 107 zuwa asibitoci daga cikinsu da akwai wasu shahidai 3 da aka fito da su daga cikin baraguzai; haka nan kuma wasu mutanen da adadinsu ya kai 247 sun jikkata.

Ya zuwa yanzu adadin wadanda su ka yi shahada tun daga ranar 7 ga watan Oktoba 2023 zuwa yanzu, sun kai dubu 53,762. Sai kuma wadanda su ka jikkata sun kai 1222, 197.

Daga sake dawo da yaki akan alummar Gaza, a ranar 18 ga watan Maris, adadin wdanda su ka yi shahada sun kai 3,613, sai kuma wadanda su ka jikkata da su ka kai 10,156.

Ma’aikatar kiwon lafiya ta Gaza ta kuma ce, da akwai wani adadi mai yawa na shahidai da suke a karkashin baraguzai da rashin kayan aiki ya hana masu aikin ceto isa gare su.

Adadin kananan yaran da su ka yi shahada tun daga fara yakin, fiye da shekara daya da rabi, sun kai 16,503.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan Boko Haram sun kashe mutum 9, skun Jikkata 4 a Borno

An kashe mutane tara tare da jikkata wasu huɗu a wani da mayakan Boko Haram suka kai yankin a Malam Fatori da ke Jihar Borno.

Gwamna Babagana Zulum, wanda baya kasar a halin yanzu, ya tura tawaga ƙarƙashin jagorancin Kwamishinan Ƙananan Hukumomi, Sugun Mai Mele, domin jajanta wa waɗanda abin ya shafa da kuma tantance halin da ake ciki.

Mai Mele ya jaddada aniyar Gwamna Zulum na jajircewa wajen tabbatar da tsaron Malam Fatori saboda muhimmancinsa.

Ya sanar da shirin tura manyan injina domin tona ramuka a kusa da hedikwatar ƙaramar hukumar don hana hare-hare nan gaba daga Boko Haram da ISWAP.

Turji: Sai ka sako mutanen da ka sace za a yi sulhu — Gwamnatin Sakkwato Sarkin Ibadan ya rasu yayin da ake shirin bikin cikarsa shekara guda a mulki

Haka nan kuma ya gargaɗi mazauna yankin kan haɗin gwiwa da ’yan tawaye, inda ya yi barazanar “sakamakon Ubangiji” ga duk masu haɗin gwiwa.

An bayar da tallafin kuɗi, inda aka bai wa duk gidan da suka asa yan uwa ₦500,000, yayin da waɗanda suka jikkata huɗu kowannensu ya samu ₦250,000.

A halin yanzu, Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Tsaro na Cikin Gida, Usman Tar, ya sanar da shirin sake tsugunar da ƙarin iyalai 3,000 da suka rasa matsugunansu a Malam Fatori, wanda hakan zai kai ga jimlar gidaje 5,000 da aka sake tsugunar da su.

Tar ya tabbatar wa mazauna yankin ci gaba da ƙoƙarin gwamnati na samar da matakan tsaro da kayan aiki don dawwamammen dawowar su, yana mai kira gare su da su ci gaba da kasancewa a faɗake tare da kai rahoton duk wani abu da ba a aminta da shi ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Reuters: Amurka Tana Da Shirin Korar Falasdinawa Daga Gaza
  • ’Yan Boko Haram sun kashe mutum 9, sun Jikkata 4 a Borno
  • ’Yan Boko Haram sun kashe mutum 9, skun Jikkata 4 a Borno
  • Mutane 21 Suka Mutu A Hatsarin Mota A Hanyar Zaria Zuwa Kano
  • Falasdinawa Kimani 635 Amurka da HKI Suka Kashe A Cibiyoyin Karban Abinci A Gaza
  • Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC
  • Al’ummar A sassan Duniya Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Goyon Bayan Falasdinawa
  • Wakilin Sin Ya Yi Jawabi Game Da Raya Hidimomi Ga Nakasassu Ta Hanyar Fasahar AI A Madadin Wakilan Kasashe Fiye Da 70
  • 2027: Ana raɗe-raɗin Sanata Lamiɗo zai fice daga APC zuwa ADC
  • Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC