Yadda Tabarbarewar Tsaro Ta Kara Yawan Yaran Da Ba Sa Zuwa Makaranta
Published: 23rd, May 2025 GMT
Bincike ya yi nuni da cewa an bar dukkan al’ummomi ba tare da ingantattun makarantu ba a jihohi kamar Borno, Yobe, da Adamawa.
Sama da makarantu 1,500 ne aka lalata tun farkon rikicin Boko Haram, inda sama da malamai 19,000 suka rasa matsugunansu, kuma da yawa ma suna fargabar komawa.
‘Yan mata suna cikin hadari, galibi ana tilasta musu auren wuri ko aikin gida ko aikin jima’i maimakon a ba su damar koyo.
Wata kwararriyaa fannin ilimi da ke zaune a Jos, Jihar Filato, Misis Peace Pernam, ta ce, “Ilimi wata hanya ce ta rayuwa mai muhimmanci da ke kawar da fatara, rage matsalar tsaro, da samar da ci gaban kasa, duk da haka, ga miliyoyin yara a yankin Arewa maso Gabas, cikin matsanancin rikici, rashin kyakkyawan shugabanci, wadanda rashin sanya hannun jari ke yanke jin dadin rayuwarsu.
Al’amarin wadannan yaran bai tsaya kadai kididdiga ba. Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya (UNICEF) ya tabbatar da abin da ba a yi tsammani ba: Nijeriya ce ta fi kowacce kasa yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a duniya. Idan ka tara uku za ka samu daya daga cikinsu ba ya zuwa makaranta, wato ba ya samun ilimin boko a halin yanzu.
“Wannan matsalar ba ta tsaya kadai ga ilimi ba, al’amari ne dake bukatar taimakon gaggawaa kasa.
Idan ba a dauki matakin gaggawa ba, Nijeriya na fuskantar afkawa hadarin kasa yin kafada da sa’anninta, wajen ci gaba sace jama’a da rashin kyakkyawar gami da kakaba wa jama’a talauci, tsatsauran ra’ayi, da rashin zaman lafiya.”
A cewar wani mai sharhi kan al’amuran jama’a, Ahmed Idris, matsalar ilimi a Nijeriya na kara ta’azzara, musamman a yankunan da ke da karancin makarantu.
Ya ce yara da yawa har yanzu suna tafiya mai nisa zuwa makaranta, idan kuma sun halarci makarantar za ka samu babu kwararrun malamai.
Wani lokaci kuma, ana samun karancin ingancin malamai.
“Rashin ingancin koyarwa ya sa dalibai ba za su iya karatu ko yin lissafi ba bayan sun shafe shekaru a makaranta, don magance wannan, dole ne gwamnati ta ba da fifiko ga Ilimi kyauta da yin amfani da fasaha don cike gibin.
Ilimi shi ne ginshikin rage talauci, aikata laifuka, da rashin aikin yi, gina hanyoyin koyar da sana’o’i da kuma samar wa ‘yan Nijeriya makoma nan gaba,” in ji shi.
Wani malami da ke zaune a Abuja, Peter Ojo, ya yi gargadin cewa Nijeriya ba za ta iya kaucewa barazanar da ke kunno kai wacce ‘yan zamani marasa ilimi ke yi ba.
A cewarsa, dangantakar ilimi da ci gaban tattalin arziki ba abu ne da za a iya musantawa ba.
Ya ce, “Ta hanyar ba da fifiko ga ilimi, kasar za ta iya canza matasanta zuwa ga samar da canji mai kyau da ci gaban kasa. Bayan haka, magance duk wata matsala ta zamantakewa ta dogon lokaci dole ne sai an bi ta hanyar ilimi.”
Ya kuma kara bayyana yadda ake fama da karancin kudade a fannin ilimi, inda kashi 7.3 cikin 100 ne kawai na kasafin kudin kasar da aka ware wa ilimi, wanda bai kai kashi 15-20 bisa 100 da hukumar UNESCO ta ba da shawarar ba.
Ya ce rashin kudi a matsayin wani muhimmin al’amari da ke taimaka wa gurbacewar ababen more rayuwa, cunkoson ajujuwa, da rashin isassun kayan koyarwa, rashin wadatar dalibai da malamai da karancin ababen more rayuwa a makarantu duk su ke haifar da wadannan matsaloli.
Sai dai ya amince da ci gaban da wasu jihohin Nijeriya suka samu a baya-bayan nan, kamar su Enugu, Jigawa, Kano, da Kaduna, wadanda suka ware sama da kashi 26 na kasafin kudinsu ga ilimi a shekarar 2025.
A ‘yan kwanakin nan, gwamnatin tarayya da na jihohi da wasu kamfanoni masu zaman kansu na kokarin ganin an shawo kan matsalar yaran da ba sa zuwa makaranta a Nijeriya. A kwanakin baya, babbar sakatariyar hukumar kula da ilimin bai daya ta kasa (UBEC), Aisha Garba, ta ce hukumar za ta fadada rajista da shigar da su cikin tsarin ilimin boko domin rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a kasar nan, musamman a yankunan karkara.
Ta kuma bayyana cewa galibin yaran da ba sa zuwa makaranta suna zaune ne a yankunan karkara kuma aksarinsu ‘ya’yan talakawa ne, inda rashin daidaiton tattalin arziki ke haifar da fatara a gidaje da dama.
Ta kuma jaddada bukatar kara bayar da shawarwari don magance muhimman kalubalen ilimi a Nijeriya.
Har ila yau, gwamnatin tarayya ta kaddamar da wani sabon shiri mai suna ‘Lumina Programme’, na magance yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a Nijeriya.
Karamar ministar ilimi, Farfesa Suwaiba Ahmad Ahmad, ta bayyana cewa shirin zai samar da ilmin karance-karance da kuma ilmin lissafi, musamman ga yara mata a cikin al’ummomin da ke da wuyar isar da sako.
A Kaduna, gwamnatin jihar ta ce za ta horas da mambobin kwamitin kula da makarantu (SBMC) 8,700 domin inganta ilimi a matakin farko a jihar.
Mukaddashin shugaban hukumar kula da ilimin bai daya ta Jihar Kaduna (KADSUBEB) Mubarak Muhammad ne ya bayyana hakan a Kaduna kwanan nan.
Har ila yau, wata kungiya mai zaman kanta (NGO) mai suna IA-Foundation, ta tara Naira miliyan 30 a taron agajin da ta gudanar kwanan nan a birnin Landan domin tallafa wa ilimin yaran da ba sa zuwa makaranta a Nijeriya.
Shugabar kungiyar ta IA-Foundation, Misis Ibironke Adeagbo, ta ce za a tura asusun ne domin taimakawa muhimman ayyukan kungiyar kai tsaye.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Tsaro yaran da ba sa zuwa makaranta a
এছাড়াও পড়ুন:
NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa
Oguntala ta bayyana cewa, ana sa ran babban ministan ma’aiktar bunkasa tattalin arziki na teku Mista Adegboyega Oyetola, zai halarci taron, wanda aka tsara za a gudanar a watan Disambar wannan shekarar a garin Ibadan.
Ta bukaci hukumar ta Hukumar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Kasa NPA, da ta yi hadaka da kungiyar domin gudanar da taron wanda ta sanar da cewa, Shugaban Hukumar ta NPA Dakta Abubakar Dantsoho ne, zai kasance babban mai gabatar da jawabi, a wajen taron kungiyar.
Kazalika, ta yi kira ga Hukumar ta NPA, da ta dauki nauyin manyan kasidun da za a gabatar da wajen taron tare da samar da ilimi kan batun da ya shafi fannin na bunkasa tattalin arziki na teku.
Shugabar ta kuma bai wa hukumar ta NPA damar da ta yi bajin koli a yayin gudnar da taron, inda kuma ta sanar wa da hukumar ta NPA cewa, ta zabo wasu daga cikin injiniyoyin NPA da ta sanya a cikin kwamtin shiye-shiyen gudanar da taron.
Ta kuma shedawa Dantsoho cewa, wasu masu masana’antu da wasu daga bangaren gwamnati da kuma wasu daga bangaren manyan makarantun kasar nan, na da burin yin hadaka da hukumar ta NPA.
“Mun sa irin kokarin da shugaban hukumar ta NPA key i, musaman wajen kara bunkasa tattalin azrikin da ke a fannin ayyukan Tashoshin Jitagen Ruwan kasar” .
“Muna sane da cewa, ba za mu iya gudanar da gagarumin atron namu, matukar ba mu samu guduanmwar da za ku iya bamu ba, domin shirya taron a acikin nasara, musamman duba da irin gudunmawar da za ku iya bayarwa,” Inji ta.
“Ba wai muna neman hukumar ta dauki nauyin mu bane, muna kawai bukatar yin hadaka da hukumar ta NPA ne , musamman duba da irin gawaurtaccen taron da muke yin yi,” A cewar shugabar.
“Fannin na bunkasa tattalin arzikin teku, abu ne da yake ci gaba da kara tumbatsa kuma abu ne, da ke da makoma mai kyau, haka fannin ne, da har yanzu, mutane ba su gama fahimtarsa ba,” Inji ta.
Ta kara da cewa, idan aka ba za daukacin bangarorin injiniyoyin zuwa rassa guda 93 da ake da su a kasar nan da kuma sauran wadanda suke a kasar waje, hakan zai kara taimaka wa, wajen kara bunkasa kasar nan.
Shugabar ta kuma bijro da batun shigar wadanda suka samu shedar kammala karatun injiniya wadanda suka samu horo daga gun kwararrun injiniyoyi suke kuma yin aiki a hukumar ta NPA.
Ta kara da cewa, bisa matakan bin ka’ida da bangaren gudanar da mulki da kungiyar ta dauka su ne, na tabbatar da duk wanda ya karaci ilimin injiniya dole ne ya kasance ya kai mataki na goma
A na sa jawabin shugaban hukumar ta NPA Dakta Abubakar Dantsoho ya sanar da cewa, kashi 70 zuwa 80 na ma’ikatan da ke aiki a hukumar ta NPA injiniyoyi ne.
Dantsoho ya kuma bai wa shugabar kungiyar tabbacin cewa, za ta yi hadaka da kungiyar ta NSE, musamman domin a kara ciyar da kasar nan gaba, inda ya buga misali da sauran kasashen duniya da suka yi hadaka da kungiyoyin injiniyoyi wanda hakan ya ba su damar samun nasara, musamam ta hanyar yin hadaka.
Shugaban ya sanar da cewa, idan aka yi hadakar da hukum
ShareTweetSendShare MASU ALAKA