Mayar Da Hankali A Aikin Farfado Da Kwararrun Asibitocin Gwamnatin Tarayyya
Published: 23rd, May 2025 GMT
Matakin da Gwamnatin ta dauka, na son yin amfani da Gidauniyar TETFund, domin yin wannan aikin, babban abin jinjinawa ne, wanda idan har ba a samu wata gazawa ba, kamar a sauran ayyukan baya, musamman duba da cewa, Giduaniyar ta samu shedar cewa, ba a santa da gazawa, wajen wanzar da ayyukan da shirye-shiyen da ta sanya a gaba, kan batun ganin an inganta karatu a jami’oin kasar.
Kazalika, Ministan ya ce, daukacin aikin shi ne, domin a dakile yawan ficewar da kwararrun Likitocin kasar ne yi ne, zuwa ketere domin neman aiki, wanda hakan zai sanya, a ciki gaba da raike su a kasar nan, domin su yi aki a cikin kasar.
A karkashin aikin, za a kuma tabbatar da an samar da kayan aiki da samar da masu da karin kudade da kuma kara inganta yanayin mai kyau, da za su gudanar da ayyukansu, na duba marasa lafiya.
Alausa ya ci gaba da cewa, daukin da za a samar a fannin na kiwon lafiyar kasar, za a samar da shi ne, ga manyan bangarorin kimiyya, samar samar da magunguna da na jinya.
A cearsa, za a wanzar da wannan zuba hannun jarin ne, a fannin na zuwa shekaru biyar wanda aka kiyasta, za a kashe kudin da ya kai Naira tiriliyan 1.5 wanda za iya cimma hakan ne, ta hanyar wanzar da shiye-shiyen.
Sai dai, tun fil azala, kalubalen da kasar ke fuskanta shi ne, na Nijeriya na yin sakaci, wajen rashin wanzar da shirye-shiyen da aka dauka
Karin wani abin takaicin shi ne, fannin kiwon lafiyar kasar, musamman a kwararrun Asibitocin, sun koma tamkar abin damauwa ga ‘yan Nijeriya da kuma su kwararrun Likitocin, duba da yadda aka yi watis da ba su kulawar da ta kamata da yawan samun aikata badakalar cin hanci da rashawa, wanda hakan ya kara durkusar da fannin na kiwon lafiyar, wanda kuma hakan ya janyo, ba sanar inganciyyar kula da kiwon lafiyar da ya dace da kuma samar da ilimantar wa.
A nan za mu iya cewa, ya kamata Gwamnati baya ga samar da kayan aiki a Asibitocin, t ya kuma zama wajbi, ta zabo wasu Makarantun horas da kwararun Likitoci domin a daga darajar Makarantun.
Kwararrun Asibitocin kasar nan dai, sun jima da lalacewa da rashin ingantattun kayan aiki duba da cewa, ba su da Gadajen kwantar da marasa lafiya da suka wuce, goma kacal.
Akasarin ‘yan Nijeriya da ke bukatar a duba lafiyarsu, suna yin tururuwa zuwa kwararrun Asibitocin kasar, amma matsalar, suna shafe awowi, domin neman Gadon da za a kwantar da su don su yi jinya.
A wasu lokacin samun Asibtin, ya danganta ne da irin karfin iko da mai bukatar yake da shi.
Domin a dakile wannan matsalar, muna kira ga Gwamnati da mahukunatn irin wadannan kwararrun Asibitocin na Gwamnati, da su tabbtar da suna tattala kudaden da ake ware masu, a cikin kasafin kudin kasa, ba wai kawai batun yiwa Asibitocin garanbawul bane, amma a samar da kayan aiki na zamani, musamman mayar da hankali kan jin dadi da walwalar kwararn Likitocin.
Hakazalika, dole ne Gwamnati ta tabbatar da wanzar da samar da ingantaccen albashi, da samar da kyakyawan yanyin aikin aiki na kwararun Likitocin kasar, wanda hakan zai ba su damar samar da sakamako mai kyau, da ake bukata a fannin.
A saboda wadannan dalilan, ya zama wajibi, Gwamnatin Tarayya da rinka yin aiki kafada da kafada da kwararrun mahukuntan kiwon lafiya da sauran amsu ruwa da tsaki domin a samar da wata manhaja kan wannan aikin tare da cimma kudurin da aka sanya a gaba, kan lokaci.
Ya kamata a zuba hannun jari wajen bai wa kwararrun Likito horo domin a inganta kwarewarsu da kuma walwalarsu.
Bugu da kari, akwai bukatar a wadatar da Asibitocin kasar da kayan aiki na zamani, musamman domin a samu damar ci gaba da duba lafiyar marasa lafiya da kuma ilimantar da kwararrun Likitocin.
Ya kuma wajaba a samar da kayaan aiki na zamani da za a rinka duba manyan larorin cuttuka, kamar irinsu, Cutar Daji, wanda hakan zai sanya, masu irin wadannan larorin, ba sai sun fita zuwa Asibicin da ke ketare, domin neman lafiya ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: kwararrun Asibitocin kiwon lafiyar da kayan aiki da kwararrun kiwon lafiya a kwararrun wanda hakan
এছাড়াও পড়ুন:
UNICEF Ya Ba Da Tallafin Kayayyakin Aiki Ga Cibiyoyin Lafiya A Kirikasamma
A wani yunkuri na inganta kula da mata masu juna biyu da sauran ayyukan kiwon lafiya a jihar Jigawa, Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF tare da hadin gwiwar Karamar Hukumar Kirikasamma sun mika kayayyakin aiki da wasu muhimman kayayyaki ga cibiyar kiwon lafiya ta farko a Kirikasamma.
Mai kula da cibiyar kiwon lafiya ta farko, Kabiru Musa, ya bayyana cewa kayayyakin sun haɗa da gadajen haihuwa, zannuwan gado, kayan aikin jinya, matashin kai da sauransu, kuma za a rarraba su zuwa wuraren kiwon lafiya a fadin karamar hukumar.
A cewarsa, kayan da UNICEF da karamar hukumar suka samar za su inganta yadda ake gudanar da ayyukan kiwon lafiya a yankin.
Yayin mika kayayyakin ga mai kula da cibiyar kiwon lafiya, shugaban karamar hukumar Kirikasamma, Alhaji Muhammad Maji Wakili Marma, ya bukaci ma’aikatan lafiya da su tabbatar da gaskiya da adalci a lokacin rabon kayan.
Haka kuma, ya yaba da kokarin Gwamna Umar Namadi da sauran abokan hulda wajen gyara cibiyoyin kiwon lafiya da gina gidajen Ungozoma a Kirikasamma da kuma fadin jihar domin inganta ayyukan kiwon lafiya.
Usman Muhammad Zaria