Matakin da Gwamnatin ta dauka, na son yin amfani da Gidauniyar TETFund, domin yin wannan aikin, babban abin jinjinawa ne, wanda idan har ba a samu wata gazawa ba, kamar a sauran ayyukan baya, musamman duba da cewa, Giduaniyar ta samu shedar cewa, ba a santa da gazawa, wajen wanzar da ayyukan da shirye-shiyen da ta sanya a gaba, kan batun ganin an inganta karatu a jami’oin kasar.

Kazalika, Ministan ya ce, daukacin aikin shi ne, domin a dakile yawan ficewar da kwararrun Likitocin kasar ne yi ne, zuwa ketere domin neman aiki, wanda hakan zai sanya, a ciki gaba da raike su a kasar nan, domin su yi aki a cikin kasar.

A karkashin aikin, za a kuma tabbatar da an samar da kayan aiki da samar da masu da karin kudade da kuma kara inganta yanayin mai kyau, da za su gudanar da ayyukansu, na duba marasa lafiya.

Alausa ya ci gaba da cewa, daukin da za a samar a fannin na kiwon lafiyar kasar, za a samar da shi ne, ga manyan bangarorin kimiyya, samar samar da magunguna da na jinya.

A cearsa, za a wanzar da wannan zuba hannun jarin ne, a fannin na zuwa shekaru biyar wanda aka kiyasta, za a kashe kudin da ya kai Naira tiriliyan 1.5 wanda za iya cimma hakan ne, ta hanyar wanzar da shiye-shiyen.

Sai dai, tun fil azala, kalubalen da kasar ke fuskanta shi ne, na Nijeriya na yin sakaci, wajen rashin wanzar da shirye-shiyen da aka dauka

Karin wani abin takaicin shi ne, fannin kiwon lafiyar kasar, musamman a kwararrun Asibitocin, sun koma tamkar abin damauwa ga ‘yan Nijeriya da kuma su kwararrun Likitocin, duba da yadda aka yi watis da ba su kulawar da ta kamata da yawan samun aikata badakalar cin hanci da rashawa, wanda hakan ya kara durkusar da fannin na kiwon lafiyar, wanda kuma hakan ya janyo, ba sanar inganciyyar kula da kiwon lafiyar da ya dace da kuma samar da ilimantar wa.

A nan za mu iya cewa, ya kamata Gwamnati baya ga samar da kayan aiki a Asibitocin, t ya kuma zama wajbi, ta zabo wasu Makarantun horas da kwararun Likitoci domin a daga darajar Makarantun.

Kwararrun Asibitocin kasar nan dai, sun jima da lalacewa da rashin ingantattun kayan aiki duba da cewa, ba su da Gadajen kwantar da marasa lafiya da suka wuce, goma kacal.

Akasarin ‘yan Nijeriya da ke bukatar a duba lafiyarsu, suna yin tururuwa zuwa kwararrun Asibitocin kasar, amma matsalar, suna shafe awowi, domin neman Gadon da za a kwantar da su don su yi jinya.

A wasu lokacin samun Asibtin, ya danganta ne da irin karfin iko da mai bukatar yake da shi.

Domin a dakile wannan matsalar, muna kira ga Gwamnati da mahukunatn irin wadannan kwararrun Asibitocin na Gwamnati, da su tabbtar da suna tattala kudaden da ake ware masu, a cikin kasafin kudin kasa, ba wai kawai batun yiwa Asibitocin garanbawul bane, amma a samar da kayan aiki na zamani, musamman mayar da hankali kan jin dadi da walwalar kwararn Likitocin.

Hakazalika, dole ne Gwamnati ta tabbatar da wanzar da samar da ingantaccen albashi, da samar da kyakyawan yanyin aikin aiki na kwararun Likitocin kasar, wanda hakan zai ba su damar samar da sakamako mai kyau, da ake bukata a fannin.

A saboda wadannan dalilan, ya zama wajibi, Gwamnatin Tarayya da rinka yin aiki kafada da kafada da kwararrun mahukuntan kiwon lafiya da sauran amsu ruwa da tsaki domin a samar da wata manhaja kan wannan aikin tare da cimma kudurin da aka sanya a gaba, kan lokaci.

Ya kamata a zuba hannun jari wajen bai wa kwararrun Likito horo domin a inganta kwarewarsu da kuma walwalarsu.

Bugu da kari, akwai bukatar a wadatar da Asibitocin kasar da kayan aiki na zamani, musamman domin a samu damar ci gaba da duba lafiyar marasa lafiya da kuma ilimantar da kwararrun Likitocin.

Ya kuma wajaba a samar da kayaan aiki na zamani da za a rinka duba manyan larorin cuttuka, kamar irinsu, Cutar Daji, wanda hakan zai sanya, masu irin wadannan larorin, ba sai sun fita zuwa Asibicin da ke ketare, domin neman lafiya ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kwararrun Asibitocin kiwon lafiyar da kayan aiki da kwararrun kiwon lafiya a kwararrun wanda hakan

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai

Shugaba Bola Tinubu ya yi wa sabbin Shugabannin Sojoji ado da karin girma domin su dace da sabbin muƙamansu. Sabbin shugabannin rundunar sojin kasar da aka yi wa ado sun hada da Laftanar Janar, wanda yanzu ya zama Janar Olufemi Olatubosun Oluyede, a matsayin Babban Hafsan Tsaro (CDS); da kuma Manjo Janar yanzu ya koma Laftanar Janar Emmanuel Undiendeye Undiendeye a matsayin Babban Hafsan Tsaro na farin kaya (CDI). Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda  Sauran su ne Manjo Janar, wanda yanzu ya zama Laftanar Janar Waidi Shaibu a matsayin Babban Hafsan Soja (COAS); Air Vice Marshal, wanda yanzu ya zama Air Marshal Kevin Aneke a matsayin Babban Hafsan Sojan Sama; da kuma Rear Admiral, wanda yanzu ya zama Vice Admiral Idi Abbas a matsayin Babban Hafsan Sojan Ruwa. Shugaba Tinubu ya sanar da maye gurbin Shugabannin Rundunar tsaron ne a ranar Juma’ar da ta gabata, wani mataki da aka danganta da bukatar sake mai da hankali da kuma karfafa tsaron kasa. Bayan haka, Shugaba Tinubu ya bukaci sabbin Shugabannin Rundunar tsaron da su dauki mataki mai tsauri kan barazanar tsaro da ke tasowa a fadin kasar, yana mai gargadin cewa ‘yan Nijeriya na tsammanin ganin sakamako, ba uzuri ba. ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda  October 30, 2025 Manyan Labarai Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC October 30, 2025 Manyan Labarai Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Jerin Gwarazan Taurarinmu
  • Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Tinubu Ya Yi Wa Shugabannin Tsaro Ado Da Sabbin Muƙamai