Ma’aikatar Tsaro Ta Fitar da Rahoton Nasarori Karkashin Shirin “Sabuwar Fata” na Shugaba Tinubu
Published: 22nd, May 2025 GMT
Ma’aikatar Tsaro ta fitar da cikakken rahoton nasarorin da ta cimma daga watan Agusta 2023 zuwa Afrilu 2025, inda ta danganta nasarorin da manufofin kamfen din Shugaba Bola Ahmed Tinubu na “Sabuwar Fata.” wato (Renewed Hope).
Wannan rahoto ya samu hadin gwiwa daga Ofishin Mai Baiwa Shugaban Kasa Shawara Kan Tsare-tsare da Hadin Kai tare da Cibiyar Tsare-tsaren Aiki ta Gwamnati (CRDCU).
Daya daga cikin manyan nasarorin da rahoton ya nuna shi ne hadin gwiwa da Ofishin Mai Baiwa Shugaban Kasa Shawara kan Tsaro (ONSA) don kirkiro da aiwatar da sabuwar manhaja ta hadin gwiwa tsakanin sojoji da fararen hula (CIMIC).
Wannan manhaja na da nufin inganta fahimta da aiki tare tsakanin jami’an tsaro da al’umma, musamman a yankunan da ke fama da rikice-rikice.
Ma’aikatar ta kuma samu ci gaba a fannonin tsare-tsaren tsaro, karfafa hadin gwiwar hukumomi, da kuma inganta iyawar sojoji wajen gudanar da ayyukan cikin gida da na waje. Wannan na cikin kokarin gwamnati na tabbatar da tsaro da ci gaban kasa.
Rahoton ya kwatanta wadannan nasarori da alkawuran da aka dauka a cikin Tsarin Aiki na “Sabuwar Fata,” yana mai nuna yadda gwamnati ke sauke nauyin da ke wuyanta.
A yayin da Najeriya ke ci gaba da fuskantar kalubalen tsaro, Ma’aikatar Tsaro ta tabbatar da kudurinta na ci gaba da kawo sauyi da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a duk fadin kasar.
Bello Wakili
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Nasarori Rahoto Sabuwar Fata Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
SON Ta Bada Shaidar Ingancin Kayayyaki Ga Wasu Kamfanoni A Kaduna
Hukumar Kula da Ingancin Kayayyaki ta Najeriya (SON) ta gudanar da bikin bayar da takardun shaidar MANCAP ga kayayyaki 31 da suka cika sharuddan inganci a ofishinta da ke Kaduna.
Taron wata babbar nasara ce ga masana’antun da abin ya shafa, duba da yadda ya kara jaddada muhimmancin tabbatar da inganci a masana’antun cikin gida na Najeriya.
A jawabin maraba da ya gabatar, Injiniya Mamza Irimiya, mai kula da ofishin SON na jihar Kaduna, ya yabawa kokarin wadanda suka sami shaidar, yana mai cewa “Samuwa ko mallakar takardar shaidar MANCAP ba abu ba ne da ake siya, tsari ne na jajircewa da kokari. Yau an karrama ku ne saboda kokarin ku, wanda hakan mataki ne farko , domin tabbatar da ingancin kayyaki abu ne da za a ci gaba da yi lokaci bayan lokaci.”
Injiniya Irimiya ya jaddada muhimmancin kirkire-kirkire da sabbin fasahohi, tare da karfafa gwiwar wadanda suka samu shaidar da su ci gaba da yin kokarin da zai kai kayayyakin su zuwa kasuwannin duniya a maimakon cikin gida kawai.
Ya bayyana cewa, shaidar tana kara wa masu amfani da kayayyakin cikin gida kwarin gwiwa kan ingancin kayayyakin Najeriya.
Wakilin Babban Daraktan SON, Dr. Ifeanyi Chukwunonso Okeke, wato Daraktan Yankin Arewa maso Yamma, Mr. Isaac Omebije Onojo, ya bayyana cewa “Bin ka’idoji a masana’antu yana da matukar muhimmanci, domin rashin yin hakan na iya jefa kasuwancin cikin barazana.Shirin MANCAP yana tabbatar da cewa kayayyakin da ake sarrafawa a Najeriya suna da inganci da aminci ga masu amfani.”
Mr. Onojo ya taya wadanda suka samu shaidar murna, yana kuma karfafa su da su ci gaba da inganta ayyukansu. Ya kuma gargadi masu masana’antu kan illar samar da kayayyaki marasa inganci, yana mai cewa hakan ba wai kawai yana cutar da masu amfani ba ne, har ma yana bata sunan masana’antun.
Ya kara da cewa, “Bin ka’idoji yana bunkasa kasuwanci tare da kare lafiyar jama’a.”
A nasa jawabin, Kwamishinan Harkokin Kasuwanci, Kirkire-Kirkire da Fasaha na jihar Kaduna ya bayyana cewa samun shaidar nan ya nuna jajircewar kamfanonin wajen kare hakkin masu amfani da tabbatar da ingancin kayayyaki.
Ya yaba wa SON bisa kokarin da suke yi wajen tabbatar da cewa kamfanoni da dama sun samu takardun shaidar domin inganta kayayyakin da ke kasuwa.
Daga cikin kamfanonin da suka samu takardar MANCAP akwai Global Care Industry Ltd., Simalox Paint and Decoration Services, Matrix Fertilizer Ltd., Euro Form, da Al-babello Trading Company Ltd., da sauransu.
Wannan nasara na da matukar muhimmanci wajen habbaka masana’antu da gamsar da bukatun kasuwa tare da taimakawa ci gaban tattalin arzikin jihar Kaduna.
Shamsuddeen Mannir Atiku