Ma’aikatar Tsaro Ta Fitar da Rahoton Nasarori Karkashin Shirin “Sabuwar Fata” na Shugaba Tinubu
Published: 22nd, May 2025 GMT
Ma’aikatar Tsaro ta fitar da cikakken rahoton nasarorin da ta cimma daga watan Agusta 2023 zuwa Afrilu 2025, inda ta danganta nasarorin da manufofin kamfen din Shugaba Bola Ahmed Tinubu na “Sabuwar Fata.” wato (Renewed Hope).
Wannan rahoto ya samu hadin gwiwa daga Ofishin Mai Baiwa Shugaban Kasa Shawara Kan Tsare-tsare da Hadin Kai tare da Cibiyar Tsare-tsaren Aiki ta Gwamnati (CRDCU).
Daya daga cikin manyan nasarorin da rahoton ya nuna shi ne hadin gwiwa da Ofishin Mai Baiwa Shugaban Kasa Shawara kan Tsaro (ONSA) don kirkiro da aiwatar da sabuwar manhaja ta hadin gwiwa tsakanin sojoji da fararen hula (CIMIC).
Wannan manhaja na da nufin inganta fahimta da aiki tare tsakanin jami’an tsaro da al’umma, musamman a yankunan da ke fama da rikice-rikice.
Ma’aikatar ta kuma samu ci gaba a fannonin tsare-tsaren tsaro, karfafa hadin gwiwar hukumomi, da kuma inganta iyawar sojoji wajen gudanar da ayyukan cikin gida da na waje. Wannan na cikin kokarin gwamnati na tabbatar da tsaro da ci gaban kasa.
Rahoton ya kwatanta wadannan nasarori da alkawuran da aka dauka a cikin Tsarin Aiki na “Sabuwar Fata,” yana mai nuna yadda gwamnati ke sauke nauyin da ke wuyanta.
A yayin da Najeriya ke ci gaba da fuskantar kalubalen tsaro, Ma’aikatar Tsaro ta tabbatar da kudurinta na ci gaba da kawo sauyi da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a duk fadin kasar.
Bello Wakili
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Nasarori Rahoto Sabuwar Fata Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Zargin Kisan Kiristoci: ’Yan majalisar Amurka sun yi amfani da bayanai marasa tushe — Gwamnati
Gwamnatin Tarayya ta ƙaryata zargin da wasu ’yan majalisar dokokin Amurka suka yi cewa ana yi wa Kiristoci kisan gilla a Najeriya.
Ministan Watsa Labarai, Mohammed Idris, ya ce wannan zargi ya ta’allaƙa ne da bayanai marasa tushe, waɗanda ba su san yanayin tsaron Najeriya ba.
“Wasu daga cikin iƙirarin da jami’an Amurka suka yi sun dogara ne da bayanai marasa inganci da tunanin cewa yawancin waɗanda ake kai wa hare-hare Kiristoci ne,” in ji Idris.
“Waɗannan miyagu (’yan ta’adda) ba su ware addini ɗaya ba, suna kai wa Kiristoci da Musulmai hari musamman a Arewacin ƙasar nan.”
Ya bayyana cewa Najeriya ƙasa ce mai yawan addinai da ke zaune lafiya tare, kuma irin waɗannan rahotanni na ƙarya na iya haddasa rikici da tayar da fitina.
“Keɓe waɗannan hare-hare da sunan wani addini abu ne mai hatsarin gaske. Najeriya ƙasa ce wadda mutane suka yadda da juna inda mutane masu addinai daban-daban ke rayuwa cikin lumana,” in ji ministan.
Idris, ya ce gwamnati na ci gaba da inganta fannin tsaro, ciki har da samar da sabbin kayan aiki da haɗin kai mai ƙarfi tsakanin hukumomin tsaro.
Ya bayyana cewa tun daga shekarar 2009, Najeriya ke yaƙi da ta’addanci da ’yan fashin daji, kuma sauye-sauyen da aka yi kwanan nan sauke Hafsoshin Tsaro na nufin inganta tsaro.
Ministan, ya ƙara da cewa gwamnati tana amfani da hanyoyin zaman lafiya ta hanyar noman abinci, samar da ayyukan yi, da shirye-shiryen tallafa wa jama’a don rage talauci da ƙarfafa haɗin kai a tsakanin al’umma.