Jami’an tsaro sun kashe ’yan ta’adda 13,000 daga 2023 zuwa yanzu —Ribadu
Published: 23rd, May 2025 GMT
Babban Mashawarcin Tsaro na Kasa, Malam Nuhu Ribadu, ya bayyana cewa an kashe ’yan ta’adda sama da 13,000 a fadin Najeriya daga lokacin da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta hau mulki a watan Mayun 2023 zuwa yanzu.
Ribadu, yayin da yake jawabi a taron Koli na Jam’iyyar APC a zauren taro na Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, ya bayyana cewa duk da an samu ci-gaba mai sosai wajen magance matsalar rashin tsaro, yanayin sarƙaƙiyar tsaro ya sa a mafi yawan lokaci jama’a ba sa iya gane waɗannan nasarori nan take.
Ribadu ya bayyana cewa an kashe jimillar ’yan tada kayar baya da ’yan fashin daji 13,543, yayin ayyuka daban-daban da sojoji da sauran hukumomin tsaro suka gudanar a faɗin ƙasar.
Ya ƙara da cewa mayaƙan Boko Haram da ISWAP 124,408 sun miƙa wuya ga jami’an tsaro.
Abin da muka sani kan labarin juyin mulki a Kwaddibuwa NAJERIYA A YAU: Dalilin ’Yan Adawa Na Ƙulla Ƙawance A Ƙarƙashin Inuwar ADC“Tun da Tinubu ya hau mulki, lamarin ya canza, inda aka kashe shugabannin ’yan ta’adda da yawa. Sojojinmu sun kashe ’yan ta’adda 13,543,” in ji Ribadu.
Ya bayyana kalubalen tsaro da gwamnatin yanzu ta gada a matsayin “wanda ke barazana ga haɗin kai da zaman lafiya da mutuncin Najeriya. Akwai manyan hare-hare, manyan barna da kuma asarar rayuka masu yawa.”
Ribadu ya lissafa manyan barazanar da suka kasance a lokacin, ciki har da “Boko Haram, ISWAP, fashi da garkuwa da mutane a Arewa maso Yamma, tayar da ƙayar baya a Kudu maso Gabas, Neja Delta da kuma rikicin makiyaya da manoma musamman a Arewa ta Tsakiya.”
Amma ya jaddada cewa duk da haka, an samu a fannin tsaro tun lokacin da gwamnatin yanzu ta hau mulki.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan ta adda Boko Haram ISWAP Tsaro yan ta adda
এছাড়াও পড়ুন:
Falasdinawa Kimani 635 Amurka da HKI Suka Kashe A Cibiyoyin Karban Abinci A Gaza
Kamfanin dillancin Labaran Assosciated Press ta bayyana cewa ana ci gaba da sukar Amurka da HKI kan cibiyoyin kisa da suka kafa a Gaza da sunan tallafawa Falasdinawa da abinci.
Labarin ya bayyana cewa ya zuwa yanzu Amurka da HKI sun kashe Falasdinawa kimani 635 wajen karban abinda suka kira taimakon abinci bayan sun sa su yunwa mai tsanani wanda zai sa su dole su fito su ne mi aminda zasu a sa a cikinsu. Amma idan sun so sojojin HKI su kashesu.
Kamfanin dillancin labaran Associeated Press ya nakalto kamfanoni Amurka guda biyu wadanda sun ce sun shigar da kara Amurka da kuma HKI kan yadda suke gudanar da cibiyoyin rabon abinda suka kira abinci a gaza, wanda bai dace ba.
Kamfanin sun bayyana cewa jami’an tsaron da Amurka da HKI suka kawo a cibiyoyin, da alamun an basu izinin su kashe falasdinawa da suka fito karban abinda suka kira a gaji. Su kuma yi amfani da yuwan da suka sa su don tilasta ,masu fita da kuma kashe su daga karshe.
Wani kamfanin rabon abincin agajin ya ce sojojin na barin wuta kan Falasdinawa hatta kan wadansa suke layin karban agajin.