Jami’an tsaro sun kashe ’yan ta’adda 13,000 daga 2023 zuwa yanzu —Ribadu
Published: 23rd, May 2025 GMT
Babban Mashawarcin Tsaro na Kasa, Malam Nuhu Ribadu, ya bayyana cewa an kashe ’yan ta’adda sama da 13,000 a fadin Najeriya daga lokacin da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta hau mulki a watan Mayun 2023 zuwa yanzu.
Ribadu, yayin da yake jawabi a taron Koli na Jam’iyyar APC a zauren taro na Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja, ya bayyana cewa duk da an samu ci-gaba mai sosai wajen magance matsalar rashin tsaro, yanayin sarƙaƙiyar tsaro ya sa a mafi yawan lokaci jama’a ba sa iya gane waɗannan nasarori nan take.
Ribadu ya bayyana cewa an kashe jimillar ’yan tada kayar baya da ’yan fashin daji 13,543, yayin ayyuka daban-daban da sojoji da sauran hukumomin tsaro suka gudanar a faɗin ƙasar.
Ya ƙara da cewa mayaƙan Boko Haram da ISWAP 124,408 sun miƙa wuya ga jami’an tsaro.
Abin da muka sani kan labarin juyin mulki a Kwaddibuwa NAJERIYA A YAU: Dalilin ’Yan Adawa Na Ƙulla Ƙawance A Ƙarƙashin Inuwar ADC“Tun da Tinubu ya hau mulki, lamarin ya canza, inda aka kashe shugabannin ’yan ta’adda da yawa. Sojojinmu sun kashe ’yan ta’adda 13,543,” in ji Ribadu.
Ya bayyana kalubalen tsaro da gwamnatin yanzu ta gada a matsayin “wanda ke barazana ga haɗin kai da zaman lafiya da mutuncin Najeriya. Akwai manyan hare-hare, manyan barna da kuma asarar rayuka masu yawa.”
Ribadu ya lissafa manyan barazanar da suka kasance a lokacin, ciki har da “Boko Haram, ISWAP, fashi da garkuwa da mutane a Arewa maso Yamma, tayar da ƙayar baya a Kudu maso Gabas, Neja Delta da kuma rikicin makiyaya da manoma musamman a Arewa ta Tsakiya.”
Amma ya jaddada cewa duk da haka, an samu a fannin tsaro tun lokacin da gwamnatin yanzu ta hau mulki.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan ta adda Boko Haram ISWAP Tsaro yan ta adda
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci Daga Yanzu
A wani rahoto da miami herald ya wallafa a jiya jumaa ya nuna cewa kasar Amurka na shirin kaiwa kasar Venuzuwela hare hare, yayin da Donald trump shugaban kasar Amurka yake musantawa cewa babu wani shiri na daukar matakin soji a kasar ta latin Amurka.
Yace gwamnatin trump ta yanke shawarar kai hari kan wasu wuraren soji a kasar, a kowanne lokaci.
Yace duk da yakin da washington ke yi kan miyagun kwayoyoi gwamnatinsa ba ta la’akari da kai hare-haren sojin kan venuzuwela yana nuna a akwai karo da juna a kalamansa na makon da ya gabata
Da manema labarai suka tambayeshi ko hare-haren da Amurka takai a yan kwanakin nan kan jiragen ruwa a yankin karebiya da aka ce suna fataucin miyagun kwayoyi na iya sanyawa akai hare hare kan venuzuwela trumpa ya amsa da cewa A’a.
A yan makwannin nan da suka gabata Trump ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta kai hari kan wuraren da suke da alaka da miyagun kwayoyi acikin venuzuwela yana mai cewa kasar za ta zama it ace ta gaba da za su daukai mataki a kanta.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Sanya Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3 October 31, 2025 HKI Na Ci Gaba Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta A Gaza Inda Take Kashe Falasdinawa October 31, 2025 An Tube Yarima Mai Jiran Gado Na Birtaniya Bayan Da Aka Tabbatar Da Laifinsa October 31, 2025 Kasashen Pakistan Da Afghanistan Sun Tsawaita Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta October 31, 2025 M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi October 31, 2025 Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda October 31, 2025 Araqchi: Gwajin Makaman Nukiliya Na Amurka Babbar Barazana Ce Ga Duniya October 31, 2025 Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan October 31, 2025 Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar October 31, 2025 Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa October 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci