Gwamnatin Tarayya ta fitar da cikakken rahoto na tsakiyar zangon mulki da ke bayyana muhimman nasarorin da Ma’aikatar Ayyuka ta Tarayya ta cimma daga watan Mayu 2023 zuwa Afrilu 2025.

Rahoton, wanda Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsare-Tsare da Daidaita Ayyuka ya gabatar, ya bayyana ci gaba mai ma’ana da aka samu a fannin gine-ginen ababen more rayuwa, musamman hanyoyi, karkashin shirin Renewed Hope Action Plan na Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Daya daga cikin manyan nasarorin da rahoton ya nuna shi ne ci gaba da aiwatar da shirin Highway Development and Management Initiative (HDMI), wanda ke amfani da tsarin haɗin gwiwa tsakanin gwamnati da masu zaman kansu (PPP). Wannan tsarin ya ba da damar janyo hannun jari daga masu zaman kansu don gyara da gina sabbin manyan hanyoyi da ke haɗa manyan birane da cibiyoyin kasuwanci a faɗin ƙasar.

Ma’aikatar Ayyuka ta kuma canja fasaha wajen gina hanyoyi daga amfani da kwalta zuwa amfani da fasahar siminti (concrete technology), wacce aka sani da jurewa dogon lokaci da rage buƙatar gyare-gyare akai-akai.

Wannan sabon tsarin yana tabbatar da cewa hanyoyin da ake ginawa yanzu za su dawwama, za su kasance masu aminci, kuma su fi araha a nan gaba.

Rahoton ya kuma nuna yadda Ma’aikatar Ayyuka ta ke kirkirar hanyoyin samun kuɗi na musamman don aiwatar da manyan ayyuka.

Hanyoyin sun haɗa da fita kasuwa don neman jari, fitar da takardun lamuni na gine-ginen ababen more rayuwa, da kuma ƙara faɗaɗa haɗin gwiwa da masu zaman kansu.

Wannan ya taimaka wajen ɗora ma’aikatar kan tafarkin da zai kai ga ingantaccen sauyi duk da ƙalubalen tattalin arziki.

“Manufar Renewed Hope ba ƙalmar kamfen ba ce kawai — tsari ne mai rai da ake aiwatarwa a kowane yanki na Najeriya,” in ji rahoton. “Ma’aikatar Ayyuka na aiki ba dare ba rana don tabbatar da cewa al’umma sun ji daɗin wannan sauyi.”

Wasu daga cikin manyan ayyukan da ake aiwatarwa ko aka kammala sun haɗa da faɗaɗa titin Legas-Ibadan, aikin titin Abuja-Kano, da sauran hanyoyin haɗin jihohi da ke da mahimmanci ga ciniki, noma da haɗin kai na ƙasa.

Masana sun bayyana cewa waɗannan nasarori na nuni da gaskiya da nufin gyara ƙasa bisa tsari da tasiri. Da sauran shekaru biyu kafin ƙarshen wannan zangon mulki, ana sa ran za a ci gaba da jan ƙasa da sauri domin samar da ci gaba mai ɗorewa.

Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsare-Tsare da Daidaita Ayyuka (CRDCU) ya jaddada cewa bin diddigin aiki da nuna gaskiya a bainar jama’a su ne ginshiƙan tsarin mulki na Renewed Hope.

Yayin da Najeriya ke ci gaba da tafiya zuwa ga zamanancewar ababen more rayuwa, Ma’aikatar Ayyuka ta Tarayya na taka rawa mai muhimmanci wajen gina tubalin ci gaban ƙasa da haɗa al’umma da juna.

Bello Wakili

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Ayyuka Nasarori

এছাড়াও পড়ুন:

Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik November 2, 2025 Daga Birnin Sin An Bude Sabon Babin Huldar Sin Da Koriya Ta Kudu November 2, 2025 Daga Birnin Sin Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Xi Ya Mika Sakon Taya Murnar Bude Babban Gidan Tarihi Na Kasar Masar
  • Ziyarar Shugaba Xi A Koriya Ta Kudu Ta Bude Babin Yaukaka Hadin Gwiwar Yankin Asiya Da Fasifik
  • Gidauniyar IRM Da KADCHMA, Ta Ƙaddamar Da Inshorar Lafiya Kyauta Ga Mutane 200 A Kaduna
  • Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka
  • Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala
  • Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede