Ma’aikatar Ayyuka Ta Bayyana Nasarorin Tsakiyar Zango Karkashin Shirin “Renewed Hope” na Shugaba Tinubu
Published: 22nd, May 2025 GMT
Gwamnatin Tarayya ta fitar da cikakken rahoto na tsakiyar zangon mulki da ke bayyana muhimman nasarorin da Ma’aikatar Ayyuka ta Tarayya ta cimma daga watan Mayu 2023 zuwa Afrilu 2025.
Rahoton, wanda Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsare-Tsare da Daidaita Ayyuka ya gabatar, ya bayyana ci gaba mai ma’ana da aka samu a fannin gine-ginen ababen more rayuwa, musamman hanyoyi, karkashin shirin Renewed Hope Action Plan na Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Daya daga cikin manyan nasarorin da rahoton ya nuna shi ne ci gaba da aiwatar da shirin Highway Development and Management Initiative (HDMI), wanda ke amfani da tsarin haɗin gwiwa tsakanin gwamnati da masu zaman kansu (PPP). Wannan tsarin ya ba da damar janyo hannun jari daga masu zaman kansu don gyara da gina sabbin manyan hanyoyi da ke haɗa manyan birane da cibiyoyin kasuwanci a faɗin ƙasar.
Ma’aikatar Ayyuka ta kuma canja fasaha wajen gina hanyoyi daga amfani da kwalta zuwa amfani da fasahar siminti (concrete technology), wacce aka sani da jurewa dogon lokaci da rage buƙatar gyare-gyare akai-akai.
Wannan sabon tsarin yana tabbatar da cewa hanyoyin da ake ginawa yanzu za su dawwama, za su kasance masu aminci, kuma su fi araha a nan gaba.
Rahoton ya kuma nuna yadda Ma’aikatar Ayyuka ta ke kirkirar hanyoyin samun kuɗi na musamman don aiwatar da manyan ayyuka.
Hanyoyin sun haɗa da fita kasuwa don neman jari, fitar da takardun lamuni na gine-ginen ababen more rayuwa, da kuma ƙara faɗaɗa haɗin gwiwa da masu zaman kansu.
Wannan ya taimaka wajen ɗora ma’aikatar kan tafarkin da zai kai ga ingantaccen sauyi duk da ƙalubalen tattalin arziki.
“Manufar Renewed Hope ba ƙalmar kamfen ba ce kawai — tsari ne mai rai da ake aiwatarwa a kowane yanki na Najeriya,” in ji rahoton. “Ma’aikatar Ayyuka na aiki ba dare ba rana don tabbatar da cewa al’umma sun ji daɗin wannan sauyi.”
Wasu daga cikin manyan ayyukan da ake aiwatarwa ko aka kammala sun haɗa da faɗaɗa titin Legas-Ibadan, aikin titin Abuja-Kano, da sauran hanyoyin haɗin jihohi da ke da mahimmanci ga ciniki, noma da haɗin kai na ƙasa.
Masana sun bayyana cewa waɗannan nasarori na nuni da gaskiya da nufin gyara ƙasa bisa tsari da tasiri. Da sauran shekaru biyu kafin ƙarshen wannan zangon mulki, ana sa ran za a ci gaba da jan ƙasa da sauri domin samar da ci gaba mai ɗorewa.
Ofishin Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsare-Tsare da Daidaita Ayyuka (CRDCU) ya jaddada cewa bin diddigin aiki da nuna gaskiya a bainar jama’a su ne ginshiƙan tsarin mulki na Renewed Hope.
Yayin da Najeriya ke ci gaba da tafiya zuwa ga zamanancewar ababen more rayuwa, Ma’aikatar Ayyuka ta Tarayya na taka rawa mai muhimmanci wajen gina tubalin ci gaban ƙasa da haɗa al’umma da juna.
Bello Wakili
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba
A bana ake bikin cika shekaru 50 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da kungiyar Tarayyar Turai ta EU, ana kuma daf da gudanar da sabon zagayen taron jagororin Sin da EU. Sakamakon hakan, jerin ayyukan cudanya a matsayin koli tsakanin sassan biyu na kara jan hankali.
A baya-bayan nan, an gudanar da dandalin tattaunawa na manyan jami’ai tsakanin Sin da EU karo na 13 a birnin Brussels na kasar Belgium. Kuma ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya gana da shugabannin EU, tare da ziyartar kasashen Jamus da Faransa. Bangaren Sin ya jaddada cewa, bunkasar tafarkin ci gaban alaka tsakanin Sin da EU ya nuna kyakkyawar dangantakar sassan biyu maimakon adawa da juna, kuma hadin gwiwarsu shi ne tushen cimma nasara tsakaninsu. Kazalika, ya yi kira ga Sin da EU da su hada karfi waje guda don samarwa duniya wani yanayi na tabbaci.
Ya ce, matsayin alakar Sin da EU na manyan karfi biyu, kuma manyan kasuwanni biyu, kana manyan wayewar kai biyu, ya shaida damar musaya da hadin gwiwa, ba gare su kadai ba, har ma da dukkanin duniya baki daya. Jimillar karfin tattalin arzikin Sin da EU ya haura daya bisa ukun na duniya baki daya, kana darajar yawan cinikayyarsu ta haura daya bisa hudun ta duniya baki daya. Sassan biyu na rike da manufar cudanyar mabambantan sassa, suna goyon bayan cinikayya marar shinge, da wanzar da tattaunawa da tsare-tsaren gudanarwa kan muhimman batutuwa, irinsu sauyin yanayi da fasahohin AI. A halin da ake ciki, rikicin siyasar yankuna na kara tsananta, an kuma shiga yakin haraji da na cinikayya. Sin da Turai na da nauyi da hakki, da ikon hada hannu waje guda don kare adalci, da nuna adawa da cin zali daga bangare guda, da nuna kin jinin baiwa kasuwa kariya. Kamar dai yadda Sin ta bayyana, idan Sin da Turai sun wanzar da tattaunawa da hadin gwiwa, zai yi wuya a kai ga yin fito-na-fito tsakanin wasu sassa. Kazalika, idan Sin da Turai sun zabi bude kofa, da hadin gwiwar cimma moriya tare, hakan zai sauya salon dunkulewar tattalin arzikin duniya. Idan Sin da Turai sun hada hannu wajen aiwatar da manufar cudanyar mabambantan sassa, duniya ba za ta tsuduma cikin yanayi na hargitsi ba. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp