Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta bayyana muhimman nasarori da ta cimma a fannin noma da tabbacin isasshen abinci, karkashin shirin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na Renewed Hope.

Rahoton rabin wa’adi na aiki daga watan Mayu 2023 zuwa Afrilu 2025, wanda Ofishin Mai Baiwa Shugaban Kasa Shawara kan Tsare-Tsare da Hadin Gwiwa ya fitar, ya bayyana ayyukan da Ma’aikatar Noma da Tsaron Abinci ta gudanar domin cika alkawurran yakin neman zaben shugaban kasa.

Daya daga cikin manyan nasarorin da aka samu a rahoton shi ne sabunta da inganta dakunan ajiya na abinci na kasa, wanda ya taimaka wajen rage karancin abinci da daidaita farashi a kasuwanni.

Ma’aikatar ta kuma kaddamar da ayyukan gina hanyoyin ban ruwa da tafkunan ruwa domin kara yawan amfanin gona a duk shekara. Bugu da kari, an gudanar da shirin share filaye masu fadi domin kara yawan filayen noma.

A wani bangare, gwamnati ta aiwatar da shirye-shiryen musamman domin tallafawa matasa da mata masu sha’awar harkar noma. An hada da horaswa, tallafin kudi, da samar da hanyoyin samun abinci da kudin shiga ga iyalai, domin rage fatara da bunkasa yankunan karkara.

Haka kuma, an mayar da hankali wajen tabbatar da cewa kayan gona na fitar kasashen waje sun cika ka’idojin lafiya da inganci na duniya. Wannan ya baiwa Najeriya damar kara samun kudin shiga daga fitar da amfanin gona.

Ma’aikatar ta kuma karfafa aiwatar da muhimman sassa na shirin National Livestock Transformation Plan (NLTP) da ke karkashinta, wanda ya hada da samar da wuraren kiwo, shuka ciyayi da kula da dabbobi. Wannan ya taimaka wajen rage rikice-rikice tsakanin manoma da makiyaya da kuma kara yawan kiwo.

Rahoton ya nuna cewa nasarorin da aka samu sun yi daidai da alkawurran da Shugaba Tinubu ya dauka a lokacin yakin neman zabe, inda ya yi alkawarin tabbatar da wadatar abinci da bunkasar tattalin arzikin kasa ta hanyar noma.

Jami’an gwamnati sun jaddada cewa za su ci gaba da aiwatar da shirye-shiryen da za su karfafa bangaren noma, su samar da ayyukan yi, da kuma bunkasa rayuwar al’umma.

Bello Wakili

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: GwamnatiNoma

এছাড়াও পড়ুন:

NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3

Hukumar da ke shirya gasar Firimiyar Nijeriya (NPFL) ta hukunta Kano Pillars FC da tarar Naira miliyan ₦9.5, tare da rage musu maki uku da ƙwallaye uku, bayan magoya bayansu sun kutsa cikin fili a yayin wasan da suka buga da Shooting Stars a filin wasa na Sani Abacha da ke Kano. Hakan ya sa NPFL ta rufe filin wasan tare da umartar cewa Pillars za ta ci gaba da buga wasanninta na gida a filin Muhammad Dikko a Katsina.

A cewar NPFL, hukuncin ya fito ne bisa dokar C1.1, wadda ke hukunta hare-haren da ake kai wa tawagar baƙi da jami’an wasa. Hukumar ta ce wannan mataki yana nufin tabbatar da tsabtace filayen wasa daga tashin hankali da rashin ladabi daga magoya baya. “Za mu zartas da dokoki duk lokacin da irin wannan hali ya faru,” in ji Davidson Owumi, shugaban aiyuka na NPFL.

Kano Pillars Ta Samu Nasarar Farko A Gasar Firimiyar Nijeriya Ta Bana Kano Pillars Ta Ƙulla Yarjejeniya Da Gidan Rediyon RFI Hausa

An ci tarar Pillars ₦1m saboda gazawa wajen samar da tsaro, da ₦1m saboda rashin shawo kan magoya baya, da ₦1m saboda jifa a cikin fili da abubuwa masu haɗari, da ₦2m saboda kai hari ga ƴan wasan Shooting Stars da jami’an wasa. Haka kuma, Pillars za ta biya ₦2m a matsayin diyya ga ƴan wasan Shooting Stars da ₦1.5m don jami’an wasa da suka ji rauni.

NPFL ta kuma nemi hukumar ƙwallon kafa ta Nijeriya (NFF) da ta sake duba cancantar wasu jami’an wasa daga wasannin Pillars da Shooting Stars, da na Nasarawa United da Rangers. Duk da haka, Kano Pillars na da damar ɗaukaka ƙara kan hukuncin, sai dai za a iya ƙara musu wani hukuncin idan ba su yi nasara ba.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Wasanni Ahmed Musa Ya Nemi Afuwar Ƙungiyar 3SC Akan Abinda Ya Faru Da ‘Yan Wasansu A Kano October 13, 2025 Wasanni Yaushe Lamine Yamal Zai Lashe Kyautar Ballon d’Or? October 12, 2025 Wasanni Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka October 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Yada Labarai Ya Bayyana Jihar Borno A Matsayin Mafi Juriya A Najeriya
  • Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu
  • An Bukaci An Bukaci Asusun JICHIMA Ya Fadada Hanyoyin Samun Kudade Baya Ga Gwamnatin Jigawa
  • Gwamnatin Tarayya Za Ta Kammala Aikin Titin Abuja–Kaduna–Kano Shekara Mai Zuwa
  • Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi
  • NPFL Ta Ci Tarar Kano Pillars ₦9.5m, Ta Rage Mata Maki 3 Da Ƙwallaye 3
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet
  • Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang
  • Kungiyar ‘Yan Dako Ta Kasa Ta Nada Sabon Sakatare A Jigawa
  • Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista