HausaTv:
2025-05-22@20:48:45 GMT

  Ma’ariv: “Isra’ila” Ta Zama Saniyar Ware A Duniya

Published: 22nd, May 2025 GMT

Jaridar ‘yan sahayoniya ta “Ma’ariv’ ta buga labarin da yake cewa; Isra’ila tana fuskantar matsalar diplomasiyya saboda ci gaba da yakin Gaza.

Jaridar ta kuma ce; A halin yanzu “Isra’ila” tana fuskantar abinda ta kira “Tsunami Na Diplomasiyya” saboda yakin da take ci gaba da yi a Gaza.

Haka nan kuma jaridar ta soki gwamnatin Netanyahu tare da bayyana ministan harkokin waje Gadion Sa’ir wanda ta ce, ba abinda ya dame shi kamar ci gaba da zama akan kujerarsa, da cewa; Ba ya fahimtar girman musifar da take tunkaro Isra’ila.

 Har ila yau, jaridar ta yi suka ga ministar sufuri Miri Rigiv da cewa saboda ta’annuti, ta ki yin furuci da cewa Isra’ila tana karkashin takunkumin zirga-zirga ta sama, kuma abu ne mai yiyuwa ta fuskanci takunkumi na ruwa.”

 Akan ministan ilimi Yoav Kish, jaridar ta ce, babu abinda yake gabansa sai rikicin siyasa akan jami’ar Tel Aviv, maimakon ya mayar da hankali akan yanke alaka da jami’oin duniya su ka yi da jami’o’in Isra’ila.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gaza : Birtaniya ta dakatar da tattaunawar cinikayya da Isra’ila

Birtaniya ta dakatar da tattaunawar cinikayya cikin ‘yanci da Isra’ila, bayan firaminista Keir Starmer ya ce ya kadu da yadda Isra’ila ke ci gaba da yakin Gaza.

Sakataren harkokin wajen Birtaniya, David Lammy ya bayyana matakin jingine batun ciniki tsakanin Birtaniya da Isra’ila, ya kuma nemi jakadan Isra’ila a Birtaniya ya bayyana a gaban Ofishin Lamurran Cikin Gidan kasar domin ya amsa tambayoyi game da yakin da kasarsa ke ci gaba da yi a Gaza.

Mista Lammy ya ce ministan da ke lura da lamurran da suka shafi gabas ta tsakiya na Birtaniya, Hamish Falconer, zai sanar da Hotovely cewa, “hana shigar da kayan agaji zuwa Gaza har na tsawo makonni 11 mugunta ce kuma babu hujjar yin hakan” .

” A yanzu muna ci gaba da shiga wani mummunan yanayi game da wannan yaki” in ji shi.

Lammy ya kara da cewa yakin da ake yi a Gaza ya haifar da nakasu ga alakar da ke tsakanin Birtaniya da Isra’ilan, sannan ya ce gwamnatin Birtaniya za ta sa takunkumi ga mutane uku ‘yan Isra’ilan wadanda ke da hannu wajen tayar da mazauna Gaza daga muhallansu.

Wannan na zuwa ne bayan da rundunar sojin Isra’ila ta sanar a makon da ya gabata cewa za ta zafafa kai hare-hare a Gaza.

A wani lamari da za’a ce irinsa ne na farkoA ranar Litinin, a cikin wata sanarwar hadin gwiwa, kasashen Canada, Faransa, da Birtaniya sun yi Allah wadai da fadada yakin da Isra’ila ke yi a Gaza tare da yin kira ga gwamnatin kasar da ta dage takunkumin da ta hana shigar da kayayyakin jin kai a Zirin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  MDD Ta Nuna Damuwa Akan Tabarbarewar Yanayin “Yan Hijira A Gabashin  Kasar Chadi
  • Sojojin Yemen Sun Kai Wa Filin Jirgin Saman “Ben Gorion” Hari Sau Biyu A Yau Alhamis
  • MDD ta yi gargadin cewa jarirai 14,000 a Gaza kan iya mutuwa idan an ci gaba da killace Zirin 
  • Babu Wata Matar Da Aka Gurfanar Saboda Wai Ta Zama Kirista – Gwamnatin Zamfara
  • Babu Wata Matar Da Aka Gurfanar Saboda Wai Ta Zama Kirista – Gwamnatin ZamfaraBabu Wata Matar Da Aka Gurfanar Saboda Wai Ta Zama Kirista – Gwamnatin Zamfara
  • Gaza : Birtaniya ta dakatar da tattaunawar cinikayya da Isra’ila
  • Sojojin Sudan Sun Sanar Da Kammala “Tsarkake” Birnin Kahartum Daga Dakarun  RSF
  • Fransa Ta Kira Yi Kasashen Turai Da Sake Bitar Alakarsu Da “Isra’ila”
  • Kasashen duniya 22 sun bukaci Isra’ila da ta dawo da agaji gaba daya a Gaza