Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Jihar Jigawa Ta Mayar da Rarar Kudi Sama da Naira Miliyan 50 Ga Maniyyatan Aikin Hajjin 2026

Daga Usman Muhammad Zaria 

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ce ya zuwa yanzu ta mayar da sama da naira miliyan 50 ga maniyyatan jihar na shekarar 2026, biyo bayan rage kudin kujerar aikin Hajji da Hukumar Alhazai ta Kasa (NAHCON) ta sanar.

Daraktan Janar na hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Dutse, babban birnin jihar.

A cewarsa, an mayar da kudaden ga maniyyatan da suka riga suka biya kudin kujerunsu ga hukumar kafin a rage farashin.

Ahmed Labbo ya ce NAHCON ta sake fasalin kudin Hajj na Yankin Arewa wanda yanzu ya kai sama da naira miliyan 7 da dubu 600 yana mai jaddada cewa mayar da kudin umarni ne daga Hukumar Alhazai ta Kasa, sakamakon gagarumin ragin da aka yi wa kujerar Hajjin shekarar 2026.

Ya jinjina wa jami’an hukumar na yankuna bisa kwazon tattara takardun  zuwa Hajj da bayanan maniyyata cikin sauri.

Yayin da yake magana kan shirye-shiryen aikin Hajjin 2026, Labbo ya bayyana cewa hukumar na aiki ba dare ba rana domin tabbatar da ingantattun tsare-tsare ga tawagar jihar a ƙasar Saudiyya.

Ya kuma yi kira ga maniyyata su tabbatar sun biya kudin kujerunsu kafin ko a ranar 24 ga Disamba, 2025.

Ahmed Labbo ya bayyana godiya ga Gwamna Umar Namadi bisa goyon baya da jajircewarsa ga hukumar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutane 9,854 na ɗauke da cutar AIDS a Yobe 
  • An Bude Taron Bikin Cika Shakaru 41 Da Kafa Kungiyar Tattalin Arziki Ta ECO A nan Tehran
  • Yawan Yahudawan Da Suke Ficewa Daga HKI Sun Nininka Har Sau 100%
  • MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar
  • Gwamnatin Kano Ta Kara Jaddada Dokar Haramcin Yin Haya da Babur a Jihar
  • ’Yan bindiga sun sace fasto da matarsa  masu ibada a Kogi 
  • Jihar Jigawa Ta Mayar da Rarar Kudi Sama da Naira Miliyan 50 Ga Maniyyatan Aikin Hajjin 2026
  • Sojoji sun ceto ’yan mata 12 da ISWAP suka sace a Borno
  • Iran ta bayyana halin da Falasdinawa ke ciki da rauni mufi da aka wa dan adam a doron kasa
  • Dalilin da na koma jam’iyyar ADC — Atiku