An kashe ma’aikatan ofishin jakadancin haramtacciyar kasar Isra’ila biyu a birnin Washington na Amurka

Kafofin yada labaran Amurka sun rawaito cewa: An kashe ma’aikatan ofishin jakadancin haramtacciyar kasar Isra’ila biyu bayan da aka harbe su a wajen dakin adana kayan tarihi na Yahudawa da ke birnin Washington D.

C. na Amurka.

Kafofin yada labaran Amurka sun rawaito sakataren tsaron cikin gida na Amurka na cewa: An kashe ma’aikatan ofishin jakadancin haramtacciyar kasar Isra’ila biyu a kusa da gidan adana kayan tarihi na Yahudawa da ke birnin Washington, inda ake gudanar da taron kwamitin Yahudawa na Amurka (AJC). Jim kadan bayan harbin, ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta sanar da cewa an kama wanda ake zargin.

Kamfanin dillancin labarai na NBC ya bayar da rahoton cewa, ya nakalto jami’ai, cewa wanda ake zargin ya yi harbin yana sanye ne da keffiyeh kuma ya yi ihun “Free Falasdinu” a lokacin da aka kama shi.

Kafofin yada labarai, sun ambato ‘yan sanda, sun bayyana wanda aka kama a matsayin Elias Rodriguez, mai shekaru 30, yana mai cewa “wanda ya yi harbin ba shi da wani tarihin aikata laifuka da zai sa ya zama abin sa ido ga jami’an tsaro.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

UNRWA : ba wani abu dake shiga Gaza in banda bama-bamai

Hukumar Ba da Agaji ta Majalisar Dinkin Duniya mai kula da ‘yan gudun hijirar Falasdinu a Gabas ta Tsakiya (UNRWA) ta yi gargadin cewa akwai yiyuwar Gaza ta fuskanci matsalar jin kai mafi muni tun watan Oktoban 2023.

A cikin wani sako da ta wallafa a shafin X, UNRWA ta ce yanzu haka makonni 11 kenan da gwamnatin Isra’ila ta hana shigar da abinci, man fetur da magunguna zuwa Gaza.

“Makonni 11, jami’an Isra’ila da gangan sun hana duk wani kayan agaji zuwa Gaza, abin da kawai ke shiga Gaza a yanzu shi ne bama-bamai.

Daruruwan Falasdinawa ne aka kashe a wannan makon yayin da gwamnatin Isra’ila ke kara kai hare-hare ta sama, in ji UNRWA.

“Zafafa hare-haren bama-bamai ta sama da kasa da na ruwa na Isra’ila ya haifar da asarar daruruwan rayuka da kuma gudun hijirar jama’a.”inji hukumar

Mataimakin sakatare mai kula da harkokin jin kai na Majalisar Dinkin Duniya Tom Fletcher ya fada jiya talata cewa jarirai 14,000 a Gaza za su iya mutuwa cikin sa’o’i 48 masu zuwa idan ba a kai musu dauki ba.

Tom Fletcher ya yi Allah-wadai da dokar hana kai kayan agaji zuwa zirin Gaza, yana mai cewa tireloli biyar ne kawai aka ba da izinin shiga a ranar Litinin, wanda ya bayyana a matsayin “digo a cikin teku.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Gamsu Da Lokaci Da Wurin Da Za A Gudanar Da Shawarwarinta Da Amurka Zagaye Na Biyar
  • Araghchi: Iran ba za ta tattauna kan batun inganta sinadarin Uranium din ta ba
  • Ma’aikatan wutar lantarki sun tsunduma yajin aiki a Kano
  • Wani Mutum Ya Kashe Matarsa Da Duka Har Lahira A Edo
  • UNRWA : ba wani abu dake shiga Gaza in banda bama-bamai
  • Yadda aka kashe dan fashi aka kama wasu 7 a Abuja
  • Hare-Haren Isra’ila Ya Hallaka Aƙalla Mutum 38 A Gaza Cikin Rabin Sa’a
  • ’Yansanda Sun Kama Wani Mutum Sanye Da Kayan Mata A Coci A Adamawa
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3, Sun Sace 26 A Zamfara