Masanan Najeriya Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwar Afirka Da Sin A Fannin Tinkarar Kalubalen Harajin Kwastam Na Amurka
Published: 23rd, May 2025 GMT
Wasu masana a tarayyar Najeriya sun jinjinawa yadda Najeriya da Sin suka daga dangantakarsu zuwa huldar abota bisa manyan tsare-tsare a duk fannoni a bara, matakin da ya tabbatar da goyon bayansu ga kokarin tinkarar kalubalen karin harajin kwastam da Amurka ke dora musu bisa radin kai.
Kwanan baya, an gudanar da taron tattaunawa kan yadda za a tinkari harajin kwastam da Amurka ke kakabawa sauran kasashe a birnin Abuja hedkwatar Najeriya, inda babban darektan cibiyar nazarin harkokin kasar Sin ta Najeriya Charles Onunaiju ya bayyana cewa, hadin gwiwar Sin da Najeriya bisa dandalin tattauna hadin kan Sin da Afirka, da shawarar “ziri daya da hanya daya” da dai sauransu, ba ingiza bunkasuwar manyan ababen more rayuwa a Afirka kadai ya yi ba, har ma ya inganta karfin Najeriya da sauran kasashen Afrika, na tinkarar kalubaloli, da barazanar da Amurka ke haifarwa duniya.
Baya ga hakan, darektan cibiyar nazarin huldar Sin da Afrika a sabon zamani a jami’ar Abuja Sheriff Ghali Ibrahim, ya ce, kasuwar Afirka na da cikakken boyayyen karfi, kuma duba da yawan al’ummar Najeriya, tana da muhimmanci matuka ga tattalin arzikin Afirka, don haka sabuwar huldar da Najeriya da Sin ke kullawa, za ta yi babban tasiri ga kyautatuwar tsarin ciniki na duniya.
Dadin dadawa, babban manajan kungiyar hadin gwiwar manoman Najeriya wato NFGCS Retson Tedheke ya ce, dabaru da basirar bunkasar kasar Sin abubuwan koyi ne masu daraja ga nahiyar Afirka, kuma za su taka rawa wajen tinkarar kalubaloli bisa hadin kai. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Afirka Ta Kudu Ta Musanta Zargin Cin Zarafin Turawa ‘Yan Kasar Fararen Fata
Shuwagabannin Amurka da Afirka ta Kudu sun yi arangama kan zargin kisan kare dangi a Afirka ta Kudu
Fadar White House ta shaida wata zazzafar musayar wuta tsakanin shugaban Amurka Donald Trump da takwaransa na Afirka ta Kudu, Cyril Ramaphosa, wanda ya musanta zargin da ake masa na cewa Pretoria na cin zarafin ‘yan kasar fararen fata.
An yi ganawar ne mako guda bayan da Trump ya yi zargin cewa gwamnatin Afirka ta Kudu na yin kisan kiyashi ga ‘yan kasarta ‘yan asalin Turai.
A yayin tattaunawar da ta samu halartar jami’ai daga bangarorin biyu, shugaban na Amurka ya bukaci ma’aikatansa da su nuna masa faifan bidiyo da ke da alaka da zargin kisan kiyashin, sannan Ramaphosa ya kuma mika wasu takardu da alamu ke da alaka da wadannan zarge-zarge.
Ramaphosa dai ya nuna natsuwa a lokacin da yake mayar da martani kan zargin, yana mai cewa manufofin gwamnatinsa gaba daya sun yi hannun riga da abin da Trump ya fada.