Miƙa makaman ’yan bindigar Katsina ya bar baya da ƙura
Published: 13th, February 2025 GMT
A karo na biyu a kasa da wata daya wasu ’yan bindiga sun mika makamansu ga sojoji, a wani kokari na samar da zaman lafiya.
Aminiya ta ruwaito yadda a a ranar 19 ga watan Janairun 2025, ’yan bindiga suka sallama makamansu da mutanen da suka yi garkuwa da su, a wani zaman sulhu da aka yi da su a yankin Ƙaramar Hukumar Batsari ta Jihar Katsina.
A gefe guda kuma wasu kuma na zargin Gwamnatin Tarayya Nana hannu wajen yin sulhu da ’yan ta’addan ta bayan fage domin a sami zaman lafiya a Jihar.
Al’ummar Batsari sun halarci taron mika malaman inda sun bayyana ra’ayoyi mabanbanta. Wasu na ganin abin yabo da da ta kamata a ba wa goyon, wasu kuma na ganin sa a matsayin tarin shayi, saboda an mayar da al’ummar da hare-haren suka shafa saniyar ware.Wani mazaunin yankin ya ce, “Ba a gayyace mu ba amma na je na ga abin da aka yi. Kimanin motoci takwas na APC da hiluxs ɗauke da sojoji da ’yan sanda da jami’an tsaron CWC da ’yan banga.
“Na ga ’yan bindigar sun miƙa wa sojoji bindigogi biyu ƙirar Machine Gun sun neman a basu damar shiga garuruwanmu da kasuwanninu ba tare da wani ƙaido ba.
“Duk da cewa ba duk makamansu suka miƙa ba, amma na yi imani abu mai kyau ne kuma ya kamata a dama da duk hukumomin tsaro,” in ji shi. Wani ɗan yankin kuma ya ce babu yadda za a yi sulhun ya yi nasara ba tare an sanya mutanen ya yankunan da abin ya shafa ba. Ya ce, “a na farkon da ka yi, kawai jerin gwanon motocin jami’an tsaro muka gani suna zuwa wurin. Shi ne wasunsu suka je, inda suka ga ’yan bindiga sun mika musu bindigogi biyu. Haka kuma aka yi a na biyun da ka yi jiya. “Amma ban je na jiyan ba, saboda ina tunanin babu abin da zai tsinana,” in ji shi. Gwamna Radda ya jaddada matsayinsa Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, wanda ya ziyarci Batsari ya jaddada matsayinsa cewa gane da sulhu da ’yan bindigar cewa gwamnatinsa ba za ta roƙe su ko ta lallashe su su miƙa makamansu ba.Ya ce “mun sha faɗa cewa babu ɗan bindigar da za mu je mu roƙe shi don a samu zaman lafiya. Amma idan su da kansu suka zo suka miƙa wuya za mu karɓe su,” in ji a yayin wani gangamin yaƙin nemba Batsari gabanin zaɓen ƙananan hukumomin jihar da za a gudanar ranar Asabar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Batsari yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Araqchi: Gwajin Makaman Nukiliya Na Amurka Babbar Barazana Ce Ga Duniya
Ministan Harkokin Wajen Iran Abbas Araghchi ya yi gargadi a matsayin martani ga sanarwar Washington na ci gaba da gwajin makaman nukiliya, yana mai kiran hakan a matsayin wani mataki na koma-baya da Rashin yin da’a ga dokokin kasa da kasa.
Wannan na zuwa ne a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Alhamis, inda ya soki Washington saboda sauya wa Ma’aikatar Tsaron kasar suna zuwa Ma’aikatar Yaki, kuma ya yi Allah Wadai da Shirin Amurka na yin gwajin makaman nukiliya, tare da bayyana hakan a matsayin yunkurin tayar da zaune tsaye da jefa duniya a cikin bala’i.
Wanda yake aikata irin wannan halayya ne ke ci gaba da yin barazanar sake kai hari kan cibiyoyin nukiliya na Iran bisa hujjar hana Iran mallakar makaman nukiliya da sunan kare kansu daga Iran domin kada ta mallaki makaman kare dangi.” in ji ministan harkokin wajen Iran.
Ya yi Allah wadai da Amurka saboda sukar da ta dade tana yi wa shirin nukiliya na zaman lafiya na Iran yayin da ita kuma take ci gaba da gwajin makamanta na nukiliya, wanda hakan ya saba wa dokokin duniya.
Shugaban Amurka Donald Trump a ranar Laraba ya bayyana cewa makaman nukiliya na Washington su ne mafi girma a duniya, kuma ya danganta wannan matsayin da gyare-gyare da aka yi a lokacin gwamnatinsa.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Masar da Eritrea Sun Tattauna Bukatar Tallafawa Kasar Sudan October 31, 2025 Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar October 31, 2025 Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa October 31, 2025 Iran ta yi fatali da kalamman IAEA Kan Shirin Nukiliyarta October 30, 2025 Trump Ya Umarci Ma’aikatar Yakin Amurka Ta koma gwajin makaman nukiliya October 30, 2025 Isra’ila ta amince da fadada matsugunai a Yammacin Kogin Jordan October 30, 2025 Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu October 30, 2025 Sudan : Kasashen duniya na tir da cin zarafi a El-Fasher October 30, 2025 Iran Ta Jaddada Bin Hanyar Diflomasiya Ko Da A Lokacin Yaki Ne Amma Ba Zata Amince Da Bin Umarni Ba October 30, 2025 Qalibaf: Amurka Tana Yaudarar Duniya Da Zaman Lafiya, Alhalin Tana Ci Gaba Da Kai Harin Wuce Gona Da Iri October 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci