Aminiya:
2025-06-15@13:44:41 GMT

Miƙa makaman ’yan bindigar Katsina ya bar baya da ƙura

Published: 13th, February 2025 GMT

A karo na biyu a kasa da wata daya wasu ’yan bindiga sun mika makamansu ga sojoji, a wani kokari na samar da zaman lafiya.

Aminiya ta ruwaito yadda a a ranar 19 ga watan Janairun 2025, ’yan bindiga suka sallama makamansu da mutanen da suka yi garkuwa da su, a wani zaman sulhu da aka yi da su a yankin Ƙaramar Hukumar Batsari ta Jihar Katsina.

Sojoji da jami’an hukumar tsaro ta DSS da sarakunan gargajiya da mazauna sun halarci zaman na ranar Lahadi a ƙauyen Kofa da ke kid da garin Batsari. A wannann karoj manyan ’yan bindiga irin su Umar Black, Abdullahi Lankai da Jijjige da Musa Dan Gandu da Abu Radda, da sauransu, waɗanda d suka adsabi yankunan Batsari da Jibia da Safana, ne suka ajiye makamainsu. Fitaccen ɗan siyasa Ahmadu Haruna Zago ya rasu Na yi nadamar yi wa Tinubu kamfe a 2023 — Ɗan Bilki Kwamanda Sani samu rabuwar kai Ajiye makaman da ’yan ta’addan suka yi ya haifar da rabuwar kai a tsakanin mutane inda wasu ke yabawa tare alaƙanta shi da tsananta ragargazar da sojoji ke wa ’yan ta’adda.

A gefe guda kuma wasu kuma na zargin Gwamnatin Tarayya Nana hannu wajen yin sulhu da ’yan ta’addan ta bayan fage domin a sami zaman lafiya a Jihar.

Al’ummar Batsari sun halarci taron mika malaman inda sun bayyana ra’ayoyi mabanbanta. Wasu na ganin abin yabo da da ta kamata a ba wa goyon, wasu kuma na ganin sa a matsayin tarin shayi, saboda an mayar da al’ummar da hare-haren suka shafa saniyar ware.

Wani mazaunin yankin ya ce, “Ba a gayyace mu ba amma na je na ga abin da aka yi. Kimanin motoci takwas na APC da hiluxs ɗauke da sojoji da ’yan sanda da jami’an tsaron CWC da ’yan banga.

“Na ga ’yan bindigar sun miƙa wa sojoji bindigogi biyu ƙirar Machine Gun sun neman a basu damar shiga garuruwanmu da kasuwanninu ba tare da wani ƙaido ba.

“Duk da cewa ba duk makamansu suka miƙa ba, amma na yi imani abu mai kyau ne kuma ya kamata a dama da duk hukumomin tsaro,” in ji shi. Wani ɗan yankin kuma ya ce babu yadda za a yi sulhun ya yi nasara ba tare an sanya mutanen ya yankunan da abin ya shafa ba. Ya ce, “a na farkon da ka yi, kawai jerin gwanon motocin jami’an tsaro muka gani suna zuwa wurin. Shi ne wasunsu suka je, inda suka ga ’yan bindiga sun mika musu bindigogi biyu. Haka kuma aka yi a na biyun da ka yi jiya. “Amma ban je na jiyan ba, saboda ina tunanin babu abin da zai tsinana,” in ji shi. Gwamna Radda ya jaddada matsayinsa Gwamnan Jihar Katsina, Dikko Umaru Radda, wanda ya ziyarci Batsari ya jaddada matsayinsa cewa gane da sulhu da ’yan bindigar cewa gwamnatinsa ba za ta roƙe su ko ta lallashe su su miƙa makamansu ba.

Ya ce “mun sha faɗa cewa babu ɗan bindigar da za mu je mu roƙe shi don a samu zaman lafiya. Amma idan su da kansu suka zo suka miƙa wuya za mu karɓe su,” in ji a yayin wani gangamin yaƙin nemba Batsari gabanin zaɓen ƙananan hukumomin jihar da za a gudanar ranar Asabar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Batsari yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya ta roƙi ƙasashen Isra’ila da Iran da su daina rikici, su zauna lafiya su sasanta tsakaninsu. 

A wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Waje ta fitar, ta bayyana damuwa kan yadda rikicin ke ƙara ta’azzara, inda ta nemi ɓangarorin biyu da su kai zuciya nesa don samar da zaman lafiya a duniya baki ɗaya.

Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung

Sanarwar ta ce faɗa da ramuwar gayya na jefa rayukan fararen hula cikin hatsari, kuma yana iya haddasa rikici mai muni a yankin Gabas ta Tsakiya, wanda hakan zai iya barazana ga tsaron duniya da kuma ci gaban tattalin arziƙi dunuya.

“Mu a matsayimmu na ƙasa mai son zaman lafiya, muna roƙon ƙasashen da ke rikici da su zauna su tattauna maimakon su ci gaba da faɗa.”

Gwamnatin Tarayya ta kuma yi kira ga ƙasashen duniya, musamman Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya, da su ɗauki matakai don hana yaɗuwar rikicin da kuma samo hanyar warware matsalar.

Sanarwar ta ƙara da cewa amfani da ƙarfin soji ba shi da amfani matuƙa, domin faɗa ba zai kawo sauƙi ba.

Najeriya ta ce a shirye ta ke ta bayar da taimako domin hana yaɗuwar rikicin da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • HOTUNA: Yadda aka yi sulhu da ƙasurgumin ɗan fashin daji Ado Aliero a Katsina
  • An Yi Zanga-zangar Nuna Goyon Baya Ga Kin Amincewa Da Bakin Haure A Amurka 
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Isra’ila da Iran su daidaita rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu
  • Iran : Halin da ake ciki ba zai iya bada damar tattaunawa da Amurka ba
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara