Aminiya:
2025-07-07@08:15:14 GMT

Ba mu tilasta wa kowa ya koma APC ba – Tinubu

Published: 23rd, May 2025 GMT

Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya caccaki masu cewa gwamnatinsa na ingiza ’yan Najeriya wajen bin tsarin jam’iyya ɗaya, yana mai cewa ba za ka iya zargi mutane kan zaɓar jam’iyya ba.

Da yake jawabi a wajen taron ƙoli na jam’iyyar APC  karo na farko da aka yi a ranar Alhamis, da ya gudana a fadar shugaban ƙasa a Abuja, shugaban ya ce “jam’iyya ɗaya ce ke mulki”.

Jami’an tsaron Zulum sun buɗe wa Boko Haram wuta a Maiduguri An ceto matar da aka yi garkuwa da ita, da kama mutum 2 a Yobe 

“Ga waɗanda har yanzu suke tunanin fita daga jam’iyyarsu, ƙasar nan taku ce, ku riƙe ta, ga masu maganar tsarin jam’iyya ɗaya, jam’iyya ɗaya ce ke mulkin Najeriya, ba za ku zargi mutanen da ke shirin ficewa a jam’iyyar ba.

“Na yi farin ciki da abin da muke da shi kuma ina tsammanin ƙari. Haka lamarin yake. Muna cikin tsarin mulkin demokraɗiyya.”

Ya ce, babu wanda zai iya tilasta wa kowa ya tsaya a inda bai so, ya ƙara da cewa APC a shirye take ta karɓi ƙarin ’yan Najeriya da ke son shiga jam’iyya mai mulki.

Ya ce, “Suna ganin jam’iyyar siyasa ta gaza, amma da jajircewarku, ba mu yi ƙasa a gwiwa ba, mu ne masu ci gaba, za mu yi sojan gona, ku ci gaba da yin aiki tuƙuru… Ina saurarenku ba su ba.

“Muna da damar da za mu sa Afirka ta kasance mai mai ci gaba, amma ina roƙonku da a ci gaba da tafiya tare. Ga waɗanda ba zan iya ba ma muƙaman siyasa ba, ku yi haƙuri, za ku yi farin cikin shiga wannan jam’iyya.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Mene ne tasirin naɗin Mataimaka na Musamman a rayuwar jama’a?

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Zaɓaɓɓun shugabannin gwamnati sukan naɗa wasu muƙarrabai don su taya su sauke nauyin da aka ɗora musu.

Wasu na zargin naɗin ba ya rasa nasaba da sakayya ga irin rawar ga waɗanda aka naɗa saboda rawar da suka taka yayin yaƙin neman zabe.

Shin irin waɗannan nade-naɗe na da wani tasiri ga rayuwar al’umma?

NAJERIYA A YAU: Shin Ko Hadakar Sabuwar Jamiyyar ADC Za Ta Fidda Wa ‘Yan Najeriya Kitse Daga Wuta? DAGA LARABA: Cutukan Da Sinadaran Yin Burodi Ke Haifarwa

Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne kan nade-naɗen masu taimaka wa shugabanni da irin tasirin da suke da shi.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NAJERIYA A YAU: Mene ne tasirin naɗin Mataimaka na Musamman a rayuwar jama’a?
  • Bincike ya nuna ’yan Najeriya ba su gamsu da gwamnatin Tinubu ba
  • Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya Ɗaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson
  • Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC
  • Tinubu ya umarci sojoji su murƙushe ’yan ta’adda a faɗin Najeriya 
  • ‘Yan Adawa Sun Dunkule A ADC Don Tunkarar Tinubu A 2027
  •  Na’im Kassim: Kare Kasa Ba Ya Da Bukatuwa Da Izinin Kowa
  • Tinubu ko ɗansa zai naɗa shugaban INEC, APC sai ta faɗi zaɓen 2027 — Dalung
  • Sojojin HKI Kimani 40 Ne Suka Halaka Ko Suka Jikata A Jiya Jumma’a A Yankin Shuja’iyya Na Birnin Gaza
  • Sin: Tsawaitar Rikicin Ukraine Ba Zai Amfani Kowa Ba