Dangote ya sake rage farashin man fetur
Published: 22nd, May 2025 GMT
Kamfanin Dangote wanda ya mallaki matatar mai ta Dangote ya sanar da sake sabon ragin farashin man fetur na N15 a gidajen da ke hulɗa da shi.
A wata sanarwa da kamfanin ya fitar a ranar Alhamis, ya ce a sakamakon wannan ragi, ‘yan Najeriya za su sayi man fetur a kan farashi kamar haka: Naira 875 kowace lita a Legas; Za a sayar Naira 885 kowace lita a yankin Kudu maso Yamma; A Arewa maso Yamma da Arewa ta Tsakiya za a sayar kan Naira 895 kowace lita; yayin da za a sayar da shi kan Naira 905 kan kowace lita a Kudu maso Gabas, Kudu maso Kudu, da Arewa maso Gabas.
Waɗannan farashin za su yi aiki ne ta duk abokan hulɗa.
An yi Jana’izar Shugaban Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Ƙasa a Zariya Zargin Satar Fasaha: Kotu ta sanya ranar yanke hukunci kan shari’ar BBCA cewar matatar, abokan huldar sun haɗa da gidajen man kamfanonin: MRS, AP, Heyden, Optima, TechnOil, da Hyde.
Matatar ta yi kira ga sauran ‘yan kasuwa da su haɗa kai da abokan hulɗarta, ta yadda za su nuna goyon bayansu ga manufofin farko na Shugaba Bola Tinubu, da ke ba da shawarar ba da fifiko ga kayayyaki da ayyuka da ake samarwa a cikin gida.
Tun lokacin da ta fara aiki, matatar man Dangote ta ci gaba da aiwatar da dabarun rage tsadar kayayyaki da nufin sauƙaƙawa ’yan Najeriya.
A watan Fabrairun 2025, kamfanin ya yi ragin farashin man fetur sau biyu, wanda ya haifar da raguwar jimillar Naira 125 kan kowace lita.
Hakan ya biyo bayan ragin kusan Naira 45 a kowace lita a watan Afrilu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: kowace lita a
এছাড়াও পড়ুন:
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Salim Sani Shehu
Jam’iyyar NNPP ta bayyana a hukumance cewa tsohon ɗan takararta na shugaban ƙasa a zaɓen 2023, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ba zai sake yin takarar shugaban ƙasa karkashin jam’iyyar a zaɓen 2027 ba.
Shugaban jam’iyyar na ƙasa, Agbo Major, ne ya bayyana hakan a ranar Asabar yayin da yake mayar da martani ga kalaman Buba Galadima, wanda ya ce Kwankwaso zai ci gaba da zama cikin jam’iyyar kuma zai tsaya takarar shugaban ƙasa a 2027.
Major ya ce jam’iyyar ta riga ta kori Kwankwaso da Galadima bisa zargin aikata laifukan cin amanar jam’iyya, don haka ba su da ikon magana da sunan NNPP, balle su wakilci jam’iyyar a a duk wani sha’anin siyasa.
“Tun da dadewa NNPP ta sallami Kwankwaso da Galadima, don haka ba su da hurumin magana da sunan jam’iyya ko amfani da ita a wajen neman wata kujera ta siyasa,” in ji shi.
Major ya jaddada cewa babu maganar bai wa Kwankwaso tikitin takarar shugaban ƙasa kai-tsaye kamar yadda aka ba shi a zaɓen 2023, wannan karon hakan ba zai maimaitu ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp