‘Yan sama jannatin kumbon Shenzhou-20 dake cikin tashar binciken sararin samaniya ta kasar Sin dake cikin da’irarta, sun kammala jerin ayyukansu na farko a wajen tashar a yau Alhamis.

Hukumar kula da ayyukan sama jannati ta kasar Sin (CMSA) ta ce, ‘yan sama jannatin da suka hada da Chen Dong da Chen Zhongrui da Wang Jie, sun yi aiki na tsawon sa’o’i 8, inda suka kammala da misalin karfe 4:49 na yamma agogon Beijing, bisa taimakon takwarorinsu dake duniyar dan Adam.

Chen Dong da Chen Zhongrui ne suka yi aiki a wajen tashar, inda suka fita ta hanyar dake jikin kumbon Tianhe. Wannan shi ne karo na farko da ‘yan sama jannati suka fita ta hanyar tun bayan da tashar ta shiga matakin gini da na aiki da bincike.

‘Yan sama jannatin sun kuma kafa na’urar kare tashar daga burbushin sararin samaniya a inda ya kamata. A baya, hannun mutum-mutumin inji ne ya kafa na’urar na wani lokaci na wucin gadi. (Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita

Shugaban kwamitin kungiyar tarayyar kasashen Afirka ta AU Mahamoud Ali Yousouf ya yabawa dangantakar dake tsakanin kasar Sin da kungiyar AU cewa, kasar Sin a matsayin aminiya ce da za a iya dogaro da amincewa da ita.

A yayin da yake karbar takardar wakilcin kasa daga sabon shugaban tawagar jakadun kasar Sin dake kungiyar AU Jiang Feng, Mahmoud Yousouf ya bayyana cewa, kungiyar AU tana son karfafa mu’amala da hadin gwiwar dake tsakaninta da kasar Sin, domin samar da tabbaci ga kasashen duniya dake fama da sauye-sauye a halin yanzu.

A nasa bangare kuma, Jiang Feng ya mika gaisuwa da fatan alheri na shugabannin kasar Sin ga shugaba Yousouf, ya kuma yaba wa kungiyar AU bisa babbar gudummawar da ta bayar ga aikin shimfida zaman lafiya da zaman karko a nahiyar Afirka, da jagorantar dunkulewar kasashen Afirka, da kuma yin kira da a nuna adalci ga kasashen Afirka da sauransu. Haka kuma, ya ce kasar Sin tana son hada kai da kungiyar AU wajen aiwatar da sakamakon da aka cimma a taron koli na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka na Beijing, tare da gina makomar al’ummomin Sin da Afirka ta bai daya. (Mai Fassara: Maryam Yang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jami’an Leken Asirin “Shabak” Na Isra’ila Sun Kama Nasir Lahham Na Tashar Talabijin din Almayadin
  • Lauyoyin Majalisar Dattawan Nijeriya Sun Ƙaryata Natasha Kan Cewa Kotu Ta Ce Ta Koma Bakin Aiki
  • Kasar Rasha Tana Ci Gaba Da Karya Kadarin Kasashen Turai A Yakin Da Suke Yi A Ukraine  
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kai Hare-Haren Wuce Gona Da Iri Kan Lardin Hodeidah Na Kasar Yemen
  • Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC
  • Akalla Mutane 52 Suka Rasa Rayukansu Saboda Ambaliyan Ruwan Sama A Jihar Texas Na Kasar Amurka
  • Muhimman Kamfanonin Jiragen Sama A Duniya Sun Farfado Da Zirga-Zirgaf Zuwa Iran
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci
  • Ma’aikatan MDD Masu Kula Da Ayyukan Makamashin Nukliya Na Kasar Iran Su Fice daga Kasar
  • Shugaban Kwamitin AU: Kasar Sin Aminiya Ce Da Za A Iya Dogaro Da Ita