Aminiya:
2025-09-17@22:10:41 GMT

Babban layin wutar lantarki ya faɗi karon farko a 2025

Published: 12th, February 2025 GMT

Babban layin wutar lantarkin Najeriya, ya faɗi a karon farko a shekarar 2025, lamarin da ya haddasa ɗaukewar wuta a wasu sassa.

Wannan matsala ta haifar da katsewar wuta a wasu sassan ƙasar, wanda ya jefa masu amfani da lantarki cikin damuwa.

Na yi nadamar yi wa Tinubu kamfe a 2023 — Ɗan Bilki Kwamanda Yadda na ƙi karɓar cin hancin N5bn a gwamnatin Tinubu – Tsohon Hadimi

Cikin wata sanarwa da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Abuja (AEDC), ya fitar a shafinsa na X, ya bayyana cewa matsalar ta faru ne da misalin ƙarfe 11:34 na safiyar ranar Laraba.

Sai dai AEDC, ya ce ana aiki tare da masu ruwa da tsaki domin tabbatar da dawo da wutar da zarar an shawo kan matsalar.

Rahotanni, sun nuna cewa yawan wutar lantarki a kan babbar tashar wutar lantarki ta ƙasa (TCN), ya ragu daga megawat 4,064.70 da misalin ƙarfe 11 na safe zuwa megawat 1,222.78 da ƙarfe 12 na rana.

“Muna mai baƙin ciki da sanar da ku cewa wata matsala ta auku a babban layin wuta na ƙasa da misalin ƙarfe 11:34 na safiyar yau, wanda ya haddasa ɗaukewar wuta a yankunanmu.

“Duk da cewa an fara dawo da wuta a hankali, muna tabbatar muku cewa muna aiki tare da hukumomin da suka dace domin maido da wutar gaba ɗaya da zarar an daidaita layin.

“Muna godiya da fahimtarku da haƙurin da kuke yi yayin da muke ƙoƙarin inganta ayyukanmu a gare ku.”

Babban layin lantarki na Najeriya na fuskantar matsalolin faɗuwa akai-akai, musamman a shekarar da ta gabata, inda hakan ke haddasa matsalolin ɗaukewar wuta a faɗin ƙasar.

Wannan na zuwa ne bayan da Najeriya ta fuskanci faɗuwar layin wutar lantarki sau 12 a shekarar 2024.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Babban Layi damuwa Ɗaukewa Najeriya Wutar Lantarki wutar lantarki

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Ambaliyar ruwa na cigaba da salwantar da dukiyoyi da rayukan al’ummomi da dama a sassa daban-daban na Najeriya.

 

Ko a farkon makon nan, hukumomi sun yi gargadin cewa akwai yiwuwar samun ambaliyar a jihohi akalla 11.

Sai dai wasu alummomin tuni suka dauki matakai don rage barnar da ambaliyar ka iya yi musu.

NAJERIYA A YAU: Masu Nau’in Jinin AS Sun Fi Masu Nau’in AA Lafiya DAGA LARABA: Dalilan Da Suka Sa Nayi Yunkurin Kashe Kaina Har Sau Uku

A kan wadannan matakai shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
  • Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • ’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO
  • KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta
  • KEDCO Ta Mayar Da Wutar Lantarki A Asibitin Aminu Kano
  • Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa
  • Mutuwar majinyata: Asibitin Aminu Kano na roƙon KEDCO ya dawo da wutar lantarki