Babban layin wutar lantarki ya faɗi karon farko a 2025
Published: 12th, February 2025 GMT
Babban layin wutar lantarkin Najeriya, ya faɗi a karon farko a shekarar 2025, lamarin da ya haddasa ɗaukewar wuta a wasu sassa.
Wannan matsala ta haifar da katsewar wuta a wasu sassan ƙasar, wanda ya jefa masu amfani da lantarki cikin damuwa.
Na yi nadamar yi wa Tinubu kamfe a 2023 — Ɗan Bilki Kwamanda Yadda na ƙi karɓar cin hancin N5bn a gwamnatin Tinubu – Tsohon HadimiCikin wata sanarwa da Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Abuja (AEDC), ya fitar a shafinsa na X, ya bayyana cewa matsalar ta faru ne da misalin ƙarfe 11:34 na safiyar ranar Laraba.
Sai dai AEDC, ya ce ana aiki tare da masu ruwa da tsaki domin tabbatar da dawo da wutar da zarar an shawo kan matsalar.
Rahotanni, sun nuna cewa yawan wutar lantarki a kan babbar tashar wutar lantarki ta ƙasa (TCN), ya ragu daga megawat 4,064.70 da misalin ƙarfe 11 na safe zuwa megawat 1,222.78 da ƙarfe 12 na rana.
“Muna mai baƙin ciki da sanar da ku cewa wata matsala ta auku a babban layin wuta na ƙasa da misalin ƙarfe 11:34 na safiyar yau, wanda ya haddasa ɗaukewar wuta a yankunanmu.
“Duk da cewa an fara dawo da wuta a hankali, muna tabbatar muku cewa muna aiki tare da hukumomin da suka dace domin maido da wutar gaba ɗaya da zarar an daidaita layin.
“Muna godiya da fahimtarku da haƙurin da kuke yi yayin da muke ƙoƙarin inganta ayyukanmu a gare ku.”
Babban layin lantarki na Najeriya na fuskantar matsalolin faɗuwa akai-akai, musamman a shekarar da ta gabata, inda hakan ke haddasa matsalolin ɗaukewar wuta a faɗin ƙasar.
Wannan na zuwa ne bayan da Najeriya ta fuskanci faɗuwar layin wutar lantarki sau 12 a shekarar 2024.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Babban Layi damuwa Ɗaukewa Najeriya Wutar Lantarki wutar lantarki
এছাড়াও পড়ুন:
Najeriya: Likitoci a Lagas Sun Shiga Yajin Aiki
Likitoci a jihar Lagos na tarayyar Najeriya sun fara yajin aiki na gargadi na kuma kwanaki 3 saboda nuna rashin amincewasu da rage hakkokinsu da kuma hanasu kudadensu wanda gwamnatin jihar take yi.
Jaridar Premium times ta Najeriya ta bayyana cewa duk tare da kokarin da ma’aikatar kiwon lafiya ta yi don kada likitocin su shiga yajin aiki amma a safiyar jiya litinin likitocin sun dakatar da ayyuka a dukkan asbitocin gwamnatin Jihar.
A bangaren kasha na jami’ar koyon aikin likita na Jami’ar Lagos marasa lafiya da dama sun fito don ganin likotocinsu amma sai aka fada masu duk sun shiga ya jin aiki. Wanta marasa lafiya wacce taki fadar sunanta ta fadawa Premium times kan cewa ta zo ganin likita amma an ce mata sai ranar 4 ga watan Augusta ta dawo. Kuma kafarta yana mata ciwo sosai.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai July 29, 2025 Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu July 29, 2025 Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta July 29, 2025 Manjo Janar Musawi: Ko Kadan Ba Mu Yarda Da Amurka Ba July 29, 2025 Araqchi: Iran Zata Mayar Da Martanin Da Ba Zai Yiwu A Boye Ba Kan Duk Wani Harin Wuce Gona Da Iri Kanta July 29, 2025 Kasar Iran Ta Musanta Yin Katsalandan A Tattaunawar Neman Tsagaita Bude Wuta A Gaza July 29, 2025 Rasha Ta Mayar Da Martani Ga Shugaban Amurka Kan Gindaya Wa’adin Kawo Karshen Yakin Ukraine July 29, 2025 Kasar Faransa Ta Yi Allah Wadai Da Harin Ta’addancin Da Aka Kai Birnin Zahedan Na Kasar Iran July 29, 2025 Wakilin Gidan Talabijin Na Al-Alam Ya Bayyana Yadda Shi Da Iyalansa Suka Rayu Kwanaki Biyu Babu Abinci A Gaza July 29, 2025 Pezeshkiya: Iran A Shirye Take Don Mu’amala Amma Bazata Bar Hakkinta Ba July 28, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci