An dakatar da ayyukan sauka a filin tashi da saukar jiragen sama na Lod na Isra’ila sakamakon makami mai linzami da aka harba daga Yemen

Kafofin yada labaran yahudawan sahayoniyya sun tabbatar da harba makami mai linzami daga kasar Yemen, lamarin da ya tabbatar da dakatar da zirga-zirgar jiragen sama zuwa da kuma tashi daga filin jirgin sama na Ben Gurion da ke Lod.

Jaridar haramtacciyar kasar Isra’ila ta Yedioth Ahronoth ta rawaito cewa: An dakatar da sauka a filin tashi da saukar jiragen sama na Lod tare da jinkirin jirage masu saukar ungulu, inda aka ce sama da yahudawan sahayoniyya miliyan guda ne suka tsere zuwa maboyar karkashin kasa sakamakon makami mai linzami da aka harba daga Yemen.

A halin da ake ciki na takunkumin hana zirga-zirgar jiragen sama da Yemen ta kakaba a filin jirgin sama na Lod, kamfanonin jiragen sama na kasa da kasa suna ci gaba da soke jigilarsu zuwa haramtacciyar kasar Isra’ila.

Jaridar ‘Isra’ila Hayom’ ta ‘yan sahayoniya ta bayar da rahoton cewa: Kamfanin jiragen saman Faransa Air France da na kasar Holland na Transavia suna tsawaita lokacin dakatar da zirga-zirgar jiragensu zuwa haramtacciyar kasar Isra’ila har zuwa ranar 24 ga watan Mayu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: jiragen sama

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar Biliyan ₦2.6bn

A wani hukunci da ya yanke a ranar Laraba, alkalin kotun, Ibrahim Karaye, ya ce soke hakkin wanda ya shigar da kara ya sabawa ka’ida, ya sabawa kundin tsarin mulkin kasa, kuma hukuncin ba shi da tushe balle makama.

 

Karaye ya ci gaba da cewa, sanarwar kwace shaidar mallakar filin a cikin wata wasika mai dauke da kwanan watan Satumba 3, 2021, daga ofishin kula da filaye na jihar Kano, an yi ta ne ba tare da an yi shari’a ta adalci ba, wanda hakan ya saba wa tanadin dokar amfani da filaye.

 

Alkalin ya ci gaba da bayyana cewa, takardar shaidar mallakar fili ta asali mai lamba LKN/COM/2017/116 [wacce aka sake shedawa a matsayin LPKN 1188], MLKN01622, da MLKN01837 – suna nan da inganci kuma sahihai.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kamfanonin jiragen sama sun tsawaita dakatar da zirga-zirgar zuwa Isra’ila
  • Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar ₦2.6bn
  • Kotu Ta Soke Umarnin Kwace Filin Asibitin Tiamin, Ta Umarci Gwamnatin Kano Ta Biya Diyyar Biliyan ₦2.6bn
  • Gaza : Birtaniya ta dakatar da tattaunawar cinikayya da Isra’ila
  • UNRWA : ba wani abu dake shiga Gaza in banda bama-bamai
  • Sojojin Sudan Sun Sanar Da Kammala “Tsarkake” Birnin Kahartum Daga Dakarun  RSF
  • Yanzu-yanzu: Tukunyar Gas Ta Fashe A Harabar Filin Wasannin Na Kasa Da Ke Gudana A Ogun
  • Yeman ta yi barazanar killace tashar jiragen ruwan Haifa ta Isra’ila
  • Sin Ta Cimma Nasarar Gwajin Jirgin Sama Samfurin AG600