An dakatar da ayyukan sauka a filin tashi da saukar jiragen sama na Lod na Isra’ila sakamakon makami mai linzami da aka harba daga Yemen

Kafofin yada labaran yahudawan sahayoniyya sun tabbatar da harba makami mai linzami daga kasar Yemen, lamarin da ya tabbatar da dakatar da zirga-zirgar jiragen sama zuwa da kuma tashi daga filin jirgin sama na Ben Gurion da ke Lod.

Jaridar haramtacciyar kasar Isra’ila ta Yedioth Ahronoth ta rawaito cewa: An dakatar da sauka a filin tashi da saukar jiragen sama na Lod tare da jinkirin jirage masu saukar ungulu, inda aka ce sama da yahudawan sahayoniyya miliyan guda ne suka tsere zuwa maboyar karkashin kasa sakamakon makami mai linzami da aka harba daga Yemen.

A halin da ake ciki na takunkumin hana zirga-zirgar jiragen sama da Yemen ta kakaba a filin jirgin sama na Lod, kamfanonin jiragen sama na kasa da kasa suna ci gaba da soke jigilarsu zuwa haramtacciyar kasar Isra’ila.

Jaridar ‘Isra’ila Hayom’ ta ‘yan sahayoniya ta bayar da rahoton cewa: Kamfanin jiragen saman Faransa Air France da na kasar Holland na Transavia suna tsawaita lokacin dakatar da zirga-zirgar jiragensu zuwa haramtacciyar kasar Isra’ila har zuwa ranar 24 ga watan Mayu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: jiragen sama

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Amurka Yace Yana Jirin Hamas Cikin Sa’o’i 24 Masu Zuwa Don Tsagaita Wuta Na Kwanaki 60

Shugaban kasar Amurka Donal Trump Ya Bayyana cewa nan da kwana guda ko sa’o’ii 24 masu zuwa ne zai sani, ko kungiyar Hamas ta amince da ‘shawararsa ta tsagaita wuta da HKI kuma ta karshe a gaza.

Shafin yanar gizo ta labarai ‘Arabnews ta kasar Saudia’ ta nakalto Trump yana fadar haka a yau jumma’a.

A wani bangare shugaban ya ce yayi magana da gwamnatin kasar Saudia dangane da fadada yarjeniyar Ibrahimia wacce ya samar da ita a shugabancinsa na baya wacce take bukatar kasashen larabawa su samar da huldar jakadanci da HKI, wanda kuma ya sami nasarar a kan wasu kasashen larabawa na yankin tekun Farisa.

Daga shekara ta 2023 ya zuwa yanzu yahudawan sun kashe falasdinawa kimani 56,000 sannan fiye da dubu 12000 suka ji rauni.

Majiyar Falasdinawan ya zuwa yansu, ta bayyana cewa fatansu shi ne tsagait wutar ta kaika ta zamam din-din din.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dattawa ta gindaya sharaɗin dawo da Sanata Natasha
  • Akalla Mutane 52 Suka Rasa Rayukansu Saboda Ambaliyan Ruwan Sama A Jihar Texas Na Kasar Amurka
  • Muhimman Kamfanonin Jiragen Sama A Duniya Sun Farfado Da Zirga-Zirgaf Zuwa Iran
  • Kungiyar Hamas Ta Sanar Da Matsayinta Kan Shirin Dakatar Da Bude Tsakaninta Da Gwamnatin Mamayar Isra’ila
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci
  • Neja: Cikin Wata 10 Ibtila’i Ya Lakume Rayuka Sama Da 400 – NSMA
  • Shugaban Amurka Yace Yana Jirin Hamas Cikin Sa’o’i 24 Masu Zuwa Don Tsagaita Wuta Na Kwanaki 60
  • An Bude Mafiya Yawan Tashoshin Jiragen Sama A Iran Bayan Tsaida Yaki
  • Jalali: Mun  Hana Fitowar Sanadarorin Nukiliya Ta Hanyar Aiki Da Ka’idojin Tsaro
  • NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku