Sanata Mai Wakiltar Kebbi Ta Tsakiya Ya Raba Kayayyakin Tallafi
Published: 22nd, May 2025 GMT
Sanata mai wakiltar Kebbi ta tsakiya, Sanata Muhammad Adamu Aleiro, ya raba wa al’ummar mazabar sa kayan tallafi da nufin ba su damar dogaro da kai.
Kayayyakin sun hada da babura 150 (Keke NAPEP), babura 114, firiza mai zafin rana guda 302, injin nika 750, famfunan ruwa mai amfani da hasken rana 500, injin dinki 800 da kuma buhunan taki 3,400.
Da yake jawabi a wajen bikin raba kayayyakin a karamar hukumar Aleiro ta jihar Kebbi, Sanata Adamu Aleiro, ya ce hakan na daga cikin romon dimokuradiyya ga al’ummar mazabarsa kadai, har ma da jihar.
Sanata Aleiro, ya lissafo wasu ayyukan da ya aiwatar a matsayin aikin mazabu a kananan hukumomi takwas na mazabarsa da suka hada da hanyoyi, lafiya, ilimi, kawar da zaizayar kasa da kuma cibiyoyin koyon sana’o’i.
Ya shawarci gwamnan jihar Kebbi, Kwamared Nasiru Idris, da ya ci gaba da daukar muhimman ayyukan titunan gwamnatin tarayya a jihar, yana mai tabbatar da cewa a matsayinsu na ‘yan majalisa za su bi diddigin irin wadannan ayyuka domin ganin gwamnatin tarayya ta biya kudaden da aka kashe.
Shima da yake jawabi a wajen rabon kayayyakin, Gwamnan Jihar Kebbi, Kwamared Nasiru Idris, ya yabawa Sanatan bisa yadda yake barbade al’ummarsa da ribar dimokuradiyya.
Gwamna Idris, ya bayar da tabbacin cewa gwamnatin sa ba ta taba hana wani dan majalisa damar samar da ayyukan mazabu ga jama’arsa ba yana mai cewa, duk wani aiki da za a kawo a Kebbi don amfanin al’ummar Kebbi ne.
Ya bukaci wadanda suka amfana da kada su sayar da kayayyakin, su yi amfani da su domin dogaro da kai.
COV/Abdullahi Tukur
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Kotu ta umarci a mayar da Sanata Natasha majalisa
Wata Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta umarci Majalisar Dattawa da ta mayar da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan, mai wakiltar Kogi ta Tsakiya.
A watan Maris, Majalisar Dattawa ta dakatar da Natasha na tsawon watanni shida, bayan wata taƙaddama da ta ɓarke tsakaninta da Shugaban Majalisar, Godswill Akpabio.
Kotu ta ci tarar Natasha N5m saboda kin bin umarninta ’Ya’yana na da ’yancin mallakar filaye a Abuja – WikeTaƙaddamar ta samo asali ne kan yadda aka canja tsarin zama a zauren majalisar.
Bayan dakatarwar, Natasha ta zargi Akpabio da yunƙurin cin zarafinta, inda ta kai ƙara Majalisar Ɗinkin Duniya kan lamarin.
A ranar Juma’a, Mai shari’a Binta Nyako ta yanke hukunci cewa dakatarwar watanni shida da aka yi wa Natasha ta yi tsanani.
Ta ce dokar da Majalisar Dattawa ta dogara da ita ba ta fayyace adadin kwanakin da za a iya dakatar da ɗan majalisa ba.
Alƙalin kotun ta ƙara da cewa, tun da ‘yan majalisa ke da kwanaki 181 kacal da suke zama a kowane zangon mulki, dakatar da ɗan majalisa tsawon wannan lokaci na nufin mutane daga yankinsa ba za su samu wakilci ba.
Mai shari’a Nyako ta ce ko da yake Majalisar Dattawa na da ikon hukunta mambobinta, amma hakan bai kamata ya kai ha hana al’umma samun wakilcinsu ba.
Don haka kotun ta umarci Majalisar Dattawa ta mayar da Natasha bakin aikinta.