Sanata mai wakiltar Kebbi ta tsakiya, Sanata Muhammad Adamu Aleiro, ya raba wa al’ummar mazabar sa kayan tallafi da nufin ba su damar dogaro da kai.

 

Kayayyakin sun hada da babura 150 (Keke NAPEP), babura 114, firiza mai zafin rana guda 302, injin nika 750, famfunan ruwa mai amfani da hasken rana 500, injin dinki 800 da kuma buhunan taki 3,400.

 

Da yake jawabi a wajen bikin raba kayayyakin a karamar hukumar Aleiro ta jihar Kebbi, Sanata Adamu Aleiro, ya ce hakan na daga cikin romon dimokuradiyya ga al’ummar mazabarsa kadai, har ma da jihar.

 

Sanata Aleiro, ya lissafo wasu ayyukan da ya aiwatar a matsayin aikin mazabu a kananan hukumomi takwas na mazabarsa da suka hada da hanyoyi, lafiya, ilimi, kawar da zaizayar kasa da kuma cibiyoyin koyon sana’o’i.

 

Ya shawarci gwamnan jihar Kebbi, Kwamared Nasiru Idris, da ya ci gaba da daukar muhimman ayyukan titunan gwamnatin tarayya a jihar, yana mai tabbatar da cewa a matsayinsu na ‘yan majalisa za su bi diddigin irin wadannan ayyuka domin ganin gwamnatin tarayya ta biya kudaden da aka kashe.

 

Shima da yake jawabi a wajen rabon kayayyakin, Gwamnan Jihar Kebbi, Kwamared Nasiru Idris, ya yabawa Sanatan bisa yadda yake barbade al’ummarsa da ribar dimokuradiyya.

 

Gwamna Idris, ya bayar da tabbacin cewa gwamnatin sa ba ta taba hana wani dan majalisa damar samar da ayyukan mazabu ga jama’arsa ba yana mai cewa, duk wani aiki da za a kawo a Kebbi don amfanin al’ummar Kebbi ne.

 

Ya bukaci wadanda suka amfana da kada su sayar da kayayyakin, su yi amfani da su domin dogaro da kai.

 

COV/Abdullahi Tukur

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

Amma ya nuna damuwa cewa jinkiri wajen aiwatar da yarjejeniyar da gwamnati ta yi da ASUU na ƙara haifar da rashin jituwa.

Ya roƙi Shugaba Tinubu, da ya sa baki kai-tsaye don kawo ƙarshen rikicin, yana mai gargaɗin cewa jinkiri wajen ɗaukar mataki na iya gurgunta ci gaban da aka samu a fannin ilimi.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai 2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa October 15, 2025 Labarai Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu October 15, 2025 Manyan Labarai ‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako October 15, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu
  • An Bukaci An Bukaci Asusun JICHIMA Ya Fadada Hanyoyin Samun Kudade Baya Ga Gwamnatin Jigawa
  • Jihar Kano Na Aikin Gyaran Cibiyoyin Lafiya Da Za Su Yi Gogayya Da Na Ƙasashen Duniya
  • Kudurorin Kafa Hukumomi 3 Sun Tsallake Karatu Na 2 A Majalisar Dokokin Jihar Jigawa
  • Araghchi : Trump bai cancanci mai samar da zaman lafiya ba yayin da yake haifar da yake-yake
  • Rashin Tsaro A Nijeriya Ba Zai Ƙare Ba Matuƙar Ba A Samar da Ayyukan Yi Da Mulki Na Adalci Ba – Amaechi
  • Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Gangamin Wayar Da Kai Kan Laifuka A Intanet
  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi ASUU Kan Yajin Aiki, Ta Ce “Babu Aiki, Babu Albashi”
  • Yajin Aikin ASUU:  Ba za mu biya duk wanda bai yi aiki ba — Gwamnatin Tarayya