Modric, ya lashe kofuna 28 da suka hada da gasar zakarun Turai 6 da Laliga 4 tun lokacin da ya koma Real daga Tottenham a shekarar 2012.

 

“Na zo ne a shekarar 2012 tare da fatan sanya rigar yan wasan da suka fi fice a duniya da kuma burin samun manyan nasarori, Real Madrid ta canza rayuwata a matsayina na dan wasan kwallon kafa da kuma mutum, ina alfahari da kasancewata a daya daga cikin mafi kyawun kulob a tarihi” inji shi.

 

Real za ta bude gasar cin kofin duniya na kungiyoyin kwallon kafa da Al-Hilal ta Saudi Arabiya a ranar 18 ga watan Yuni, sannan kuma za ta kara da Pachuca ta Mexico da RB Salzburg ta Austria a matakin rukuni.

 

Modric ya ci kwallaye biyu sannan ya taimaka aka ci shida a wasanni 34 da ya buga a gasar ta Sifaniya a kakar wasa ta bana, yayin da Barcelona ta lashe gasar.

 

Wasan na ranar Asabar, shi ne na karshe da Ancelotti zai jagoranci Real, inda aka ruwaito kocin Bayer Leverkusen Xabi Alonso  zai maye gurbin kocin dan kasar Italiya, shugaban kulob din Florentino Perez. A cikin wata sanarwa da ya fitar yana cewa, “Modric zai kasance har abada a cikin zukatan dukkan Madridistas a matsayin dan wasan kwallon kafa na musamman kuma abin koyi wanda a ko da yaushe ya kasance yana kunshe da kimar Real Madrid.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Imam Khaminae Ya Halarci Makokin Ashoora A Gidansa A Tehran

Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminae ya halarci zaman makokin da aka gudanar a hussainiyar Imam Khomaini (q) da cikin gidansa a nan birnin Tehran a daren Ashoorah a jiya Asabar da yamma.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Hujjatul Islam Masaoud Ali wanda ya karanta makokin yana fadar cewa, kasar Iran zata dauki darasi daga Imam Hussain (a) na rashin mika kai da azzalumai.

Ya kuma bayyana yunkurin da Iraniyawa suke yi a halin yansu yana daga cikin gwagwarmayan duniya don fuskantar azzaluman duniya karkashin jagorancin HKI da Amurka.  

Ya kuma kara da cewa musulunci ne yake gaba da gaba da kafircin duniya a cikin yakin kwanaki 12 wanda HKI da Amurka suka jagoranta kan JMI. Kuma wannan yunkirin da sauran masu gwagwarmaya a duniya zasu ci gaba da gwagwarmaya tare da jagorancin Imam Sayyid Aliyul Khaminae. Wannan dai shi ne bayyanar Jagoran a karon farko bayan yakin kwanaki 12.

Malamin ya kara da cewa, iraniyawa ba zasu mika kai ba har zuwa nasara kamar yadda muka koya daga Imam Hussain (a) hakan a ranar Ashoorah.

A lokacinda Mahmoud Karimi zai karanta makokin an ga Imam Khaminae (H) yana fadawa Karimi wani abu a kunnensa , inda daga baya Karimin ya bayyana cewa ya umurce shi y ace, kasata zaki wanzu a zuciyata da raina.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko
  • Arsenal Ta Kammala Daukar Martin Zubimendi Daga Real Sociedad
  • Al’ummar A sassan Duniya Sun Gudanar Da Zanga-Zangar Goyon Bayan Falasdinawa
  • Kofin Duniya: Real Madrid Za Ta Fara Da PSG A Semi Final
  • Imam Khaminae Ya Halarci Makokin Ashoora A Gidansa A Tehran
  • Muhimman Kamfanonin Jiragen Sama A Duniya Sun Farfado Da Zirga-Zirgaf Zuwa Iran
  • Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega
  • In Sin Da Turai Sun Yi Hadin Gwiwa, Duniya Ba Za Ta Tsunduma Cikin Yanayi Na Hargitsi Ba
  • Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya
  • NUC Da Shugabannin Makarantu Sun Yi Kira A Sanya Tsarin Kere-kere A Jami’o’in Nijeriya