Aminiya:
2025-05-22@22:24:44 GMT

An kama wani matashi da ya yi shigar mata a Adamawa

Published: 22nd, May 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Adamawa ta kama wani mai suna Mohammed Umar mai shekara 19, mazaunin wata unguwa da ake kira hanyar Abuja a ƙaramar hukumar Yola ta Kudu bisa laifin sanya tufafi da shigar mata.

Kakakin rundunar ’yan sandan, SP Suleiman Ngoruje, a wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba ya bayyana cewa, mutumin yana ta kai-kawo a cikin harabar cocin Ngurore Lutheran Church of Christ Nigeria.

Dangote ya sake rage farashin man fetur An yi Jana’izar Shugaban Ƙungiyar Masu Shirya Finafinai ta Ƙasa a Zariya

“Kamen matashi ya biyo bayan rahoton da wani mazaunin garin (da aka sakaya sunansa) ya kai hedikwatar ’yan sanda ta Ngurore, bayan ya lura da sintirin wanda ake zargin a cikin harabar cocin.”

A cewar sanarwar, Kwamishinan ’yan sandan Jihar Adamawa, Dankombo Morris, ya bayar da umarnin a mayar da batun zuwa sashin binciken manyan laifuka na Jihar, da ke Yola, domin gudanar da sahihin bincike.

“Rundunar ta ci gaba da jajircewa wajen tabbatar da tsaron jama’a, da zaman lafiyar jama’a da kuma ƙarfafa wa mazauna yankin gwiwa da su sanya ido tare da bayar da rahotannin wasu da ake yi zargi ga ‘yan sanda kan lokaci,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Adamawa

এছাড়াও পড়ুন:

DSS ta kama ɗan bindiga a cikin maniyyata aikin Hajji a Sakkwato

Dubun wani ɗan bindiga ta cika a yayin da yake shirin shiga jirgi tare da sauran maniyyata aikin Hajji a Jihar Sakkwato.

Jami’an hukumar tsaro ta DSS sun kama ɗan ta’addan mai suna Sani Galadi ne a yayin da ake yi wa maniyyata tantancewar ƙarshe kafin hawa jirgi zuwa Ƙasa Mai Tsarki a Filin Jirgi na Sultan Abubakar da ke jihar.

An kama shi ne a safiyar ranar Litinin, washegarin da jami’an tsaro suka kama wani ɗan bindiga yana yana shirin hawa mota zuwa filin jirgin sama na Abuja domin zuwa aikin Hajji.

Ɗan bindigar da aka kama a Abuja, ya kasance jami’an tsaro na nemansa kan ayyukan garkuwa da mutane a Babban Birnin Tarayya Abuja da kuma Jihar Kogi.

An kama matar ɗan ta’adda Ado Aliero da mahaifiyarsa a cikin maniyyata a Saudiyya An cimma matsaya kan dakatar da haska fina-finai 22 a Kano Yadda Boko Haram ta kashe manoma 90 a Borno cikin wata 5

Wani babban jami’in tsaro a Sakkwato ya shaida wa wakilinmu cewa ana yi wa Sani Galadi tambayoyi kuma yana ba da muhimman bayanai kafin a gurfanar da shi a kotu.

Gane da tambayar da wakilin namu ya yi masa kan yadda aka yi dan bindigar ya samu tantancewa domin zuwa aikin Hajji, sai jami’in ya sanda da cewa, “sai ka tambayi hukumomin da abin ya shafa.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An ceto matar da aka yi garkuwa da ita, da kama mutum 2 a Yobe 
  • Wani Mutum Ya Harbe Ma’aikatan Ofishin Jakadancin Isra’ila A Birnin Washington Na Amurka
  • Boko Haram: Majalisar Dattijai Ta Amince Da Kafa Sansanin Sojoji A Hong Ta Jihar Adamawa
  • Sharhin Bayan Labarai: Iran Zata Ci Gaba Da Tashe Uranium Tare Da Yarjeniya Ko Babu Ita
  • ’Yan sanda sun cafke ’yan fashi 6, sun ƙwato motocin sata 4 a Kano
  • Yadda aka kashe dan fashi aka kama wasu 7 a Abuja
  • An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya
  • ’Yansanda Sun Kama Wani Mutum Sanye Da Kayan Mata A Coci A Adamawa
  • DSS ta kama ɗan bindiga a cikin maniyyata aikin Hajji a Sakkwato