Jami’an tsaron Zulum sun buɗe wuta kan Boko Haram a Maiduguri
Published: 22nd, May 2025 GMT
Jami’an tsaro da ke raka ayarin motocin Gwamnan Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum sun buɗe wuta kan ’yan Boko Haram a hanyarsu daga Gamboru Ngala zuwa Maiduguri bayan wani rangadi na kwanaki uku.
Kodayake ba a san dalilin ’yan ta’addan ba, amma jami’an tsaron ayarin motocin sun bi su inda suka yi ta musayar wuta na kusan rabin sa’a tsakanin ƙarfe 12:50 na rana zuwa ƙarfe 1:30 na rana.
Gwamnan ya zagaya ta wasu ƙananan hukumomin ne sakamakon hare-haren da ‘yan ta’addan suka kai musu, babu tabbas ko gwamnan na cikin ayarin motocin.
Wata majiya da ke cikin tawagar ta tabbatar wa da wakilinmu faruwar lamarin a wata tattaunawa ta wayar tarho.
Gwamnan ya je garin Wulgo ne tare da tawagarsa domin duba halin da tsaro ke ciki.
“A kan hanyarmu ta zuwa Maiduguri, bayan mun tashi daga Wulgo, lamarin ya faru,” in ji wata majiya.
Sautin harbe-harbe da aka yi ba zato ba tsammani ya haifar da firgici a cikin ayarin motocin, inda wasu ke ganin cewa harin kwanton ɓauna ne wadda ya sa ayarin motocin sun yi karo da ’yan ta’addar.
Wata majiya ta ce, ‘yan ta’addar sun harba makamin roka wanda bai fashe ba a lokacin da gwamnan ke jawabi.
‘Ɗaya daga cikin jami’an tsaro ya hango wani makamin roka da ’yan ta’addan suka harba a lokacin da gwamnan ke magana ga jama’a wanda ya sanar da tawagar da su bar wurin, akan hanyarsu ta fita ‘yan ta’addan sun yi artabu da jami’an tsaro,” in ji majiyar.
Jami’an tsaron da ke cikin ayarin motocin sun buɗe musu wuta tare da tarwatsa su bayan sun yi musayar wuta.
Wata majiya kuma ta ce ‘Alhamdu lillah, yanzu mun dawo Maiduguri.’
A cikin wannan batakashi majiyar da ke ayarin na cewa wasu daga cikin rundunar haɗin gwiwa ta farar hula da wasu mafarauta waɗanda har yanzu ba a tantance adadinsu ba sun samu raunuka.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Babagana Umara Zulum ayarin motocin yan ta addan
এছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikatar Tsaro Ta Fitar da Rahoton Nasarori Karkashin Shirin “Sabuwar Fata” na Shugaba Tinubu
Ma’aikatar Tsaro ta fitar da cikakken rahoton nasarorin da ta cimma daga watan Agusta 2023 zuwa Afrilu 2025, inda ta danganta nasarorin da manufofin kamfen din Shugaba Bola Ahmed Tinubu na “Sabuwar Fata.” wato (Renewed Hope).
Wannan rahoto ya samu hadin gwiwa daga Ofishin Mai Baiwa Shugaban Kasa Shawara Kan Tsare-tsare da Hadin Kai tare da Cibiyar Tsare-tsaren Aiki ta Gwamnati (CRDCU).
Daya daga cikin manyan nasarorin da rahoton ya nuna shi ne hadin gwiwa da Ofishin Mai Baiwa Shugaban Kasa Shawara kan Tsaro (ONSA) don kirkiro da aiwatar da sabuwar manhaja ta hadin gwiwa tsakanin sojoji da fararen hula (CIMIC).
Wannan manhaja na da nufin inganta fahimta da aiki tare tsakanin jami’an tsaro da al’umma, musamman a yankunan da ke fama da rikice-rikice.
Ma’aikatar ta kuma samu ci gaba a fannonin tsare-tsaren tsaro, karfafa hadin gwiwar hukumomi, da kuma inganta iyawar sojoji wajen gudanar da ayyukan cikin gida da na waje. Wannan na cikin kokarin gwamnati na tabbatar da tsaro da ci gaban kasa.
Rahoton ya kwatanta wadannan nasarori da alkawuran da aka dauka a cikin Tsarin Aiki na “Sabuwar Fata,” yana mai nuna yadda gwamnati ke sauke nauyin da ke wuyanta.
A yayin da Najeriya ke ci gaba da fuskantar kalubalen tsaro, Ma’aikatar Tsaro ta tabbatar da kudurinta na ci gaba da kawo sauyi da tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a duk fadin kasar.
Bello Wakili